Connect with us

Ilimi

Bukin Sallah: Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Bukaci A Ba Mata Dama Su Nemi Ilimi

Published

on

Mai martaba Sarkin Kauru ta jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci jama’ ar yankin su hada kai suyi aiki tare don dakile matsalar tsaron da yankin ke fuskanta a yanzu.

A sakon sa na barka da sallah a fadarsa da ke Kauru, Mai Martaba Sarki ya nuna matukar famuwarsa akan matslaar masu garkuwa da mutane da ke kara habaka da satar amfani gona da wasu ayukkan badala a wannan yankin.

Alhaji Zakari Ya’u ya zayyano irin kalubalen da wannan matsalar ke haifarwa tsakanin al’umma tare da kira da kakkausar murya na a dauki matakin maganinta gaba daya.

Ya Kuma bayyana irin mahimmancin hadin kan al’umma akan wannan don kawo karshensa sannan ya umurci dukkanin masu rike da sarautu suyi aiki da mutanensu tare da jami’an tsaro don samo hanyar dikile wannan muguwar ta’ada.

Mai Martaba Ya’u na II yace akwai bukatar hada karfi da karfe wajen Kare rayuka da dukiyoyi da kuma fitar da al’umma daga wannan sabuwar matsala.

Bugu da kari Banda maganar tsaro, mai martaba ya kuma tabo tare da bayyana muhimmamcin kula da ilimin ‘ya’ya mata tare da Kiran a kara basu dama suje makaranta.

Sarkin Kauru Zakari Ya’u Usman II da Malam Yusuf Zubairu (Tambarin Kauru)

Sannan yayi bayanin cewa gudummuwar da ilini ke bayarwa wajen ba jama’a damar dogara DA Kai da Kuma habakar tattalin arzikin da ci gaba.

Sannam mai Martaban bai tsaya nan ba sai da kawo irin mahimmancin da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samarawa mabanbantan al’umma don haka ya bukaci a hada kai ayi aikin bunkasa yankin Kauru.

Ya Kuma jawo hankalin al’ummarsa game da mahimmancin zuwa asibiti don duba lafiya.

Radio Nigeria kaduna ya bada labarin cewa sakon mai martaba na sallah karama ya nuna irin yunkurin da yake wajen maganin matsalolin da jama’ar masarautar ke fuskanta, inda ya bayyana aiki tare ta bangaren ilimi, zaman lafiya da harkokin kula da lafiya a matsayin jigon ci gaban da ake bukata.

Sakataren masarautar Kauru, Mal Muhammad Sani Suleiman, (Dan’s buran Kauru)

 

Hakama Sakataren masarautar Kauru Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya mika sakonsa na taya murna ga mi martaba Sarki Kauru game da cikar sa shekara 3 akan mulki.

Sakon Dan Buran na Kauru ya nuna irin godiya da yadda tsarin shugabancin mai martaba da irin gudummuwar da ya ke bayarwa ga bunkasar al’ummar yankin a wadannan shekarun 3.

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai16 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai18 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai19 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi19 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara