Ilimi
Bukin Sallah: Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Bukaci A Ba Mata Dama Su Nemi Ilimi
Mai martaba Sarkin Kauru ta jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci jama’ ar yankin su hada kai suyi aiki tare don dakile matsalar tsaron da yankin ke fuskanta a yanzu.
A sakon sa na barka da sallah a fadarsa da ke Kauru, Mai Martaba Sarki ya nuna matukar famuwarsa akan matslaar masu garkuwa da mutane da ke kara habaka da satar amfani gona da wasu ayukkan badala a wannan yankin.
Alhaji Zakari Ya’u ya zayyano irin kalubalen da wannan matsalar ke haifarwa tsakanin al’umma tare da kira da kakkausar murya na a dauki matakin maganinta gaba daya.
Ya Kuma bayyana irin mahimmancin hadin kan al’umma akan wannan don kawo karshensa sannan ya umurci dukkanin masu rike da sarautu suyi aiki da mutanensu tare da jami’an tsaro don samo hanyar dikile wannan muguwar ta’ada.
Mai Martaba Ya’u na II yace akwai bukatar hada karfi da karfe wajen Kare rayuka da dukiyoyi da kuma fitar da al’umma daga wannan sabuwar matsala.
Bugu da kari Banda maganar tsaro, mai martaba ya kuma tabo tare da bayyana muhimmamcin kula da ilimin ‘ya’ya mata tare da Kiran a kara basu dama suje makaranta.
Sannan yayi bayanin cewa gudummuwar da ilini ke bayarwa wajen ba jama’a damar dogara DA Kai da Kuma habakar tattalin arzikin da ci gaba.
Sannam mai Martaban bai tsaya nan ba sai da kawo irin mahimmancin da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samarawa mabanbantan al’umma don haka ya bukaci a hada kai ayi aikin bunkasa yankin Kauru.
Ya Kuma jawo hankalin al’ummarsa game da mahimmancin zuwa asibiti don duba lafiya.
Radio Nigeria kaduna ya bada labarin cewa sakon mai martaba na sallah karama ya nuna irin yunkurin da yake wajen maganin matsalolin da jama’ar masarautar ke fuskanta, inda ya bayyana aiki tare ta bangaren ilimi, zaman lafiya da harkokin kula da lafiya a matsayin jigon ci gaban da ake bukata.
Hakama Sakataren masarautar Kauru Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya mika sakonsa na taya murna ga mi martaba Sarki Kauru game da cikar sa shekara 3 akan mulki.
Sakon Dan Buran na Kauru ya nuna irin godiya da yadda tsarin shugabancin mai martaba da irin gudummuwar da ya ke bayarwa ga bunkasar al’ummar yankin a wadannan shekarun 3.
Yusuf Zubairu
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato