Connect with us

Ilimi

An Bukaci Ayi Gyara A Manhajar Ilimin Kasan Nan.

Published

on

Babban limamin Bauchi ya yi kira da ayi gyara a manhajar tsarin ilmi don dakile rashin aikin yi a tsakanin dimbin matasa a kasar nan

Alhassan Usman Bauchi

Babban Limamin Masallacin Bauchi, Imam Bala Ahmad Baban-Inna, ya bukaci gwamnatoci a dukkanin matakai da su gyara manufofin ilimi game da horar matasa sana’o’i don magance matsalar rashin aikin yi a fadin kasar.

Imam Ahmad Baban Inna ya yi wannan kiran ne a cikin hudubarsa jim kadan bayan ya jagoranci raka’o’in biyu na Sallar Idi karama wadda aka gudanar babban Massalaci Idi na Bauchi da ke Kofar Idi a cikin a cikin garin Bauchi.

Babban Limamin Bauchi, kenan Imam Ahmad Baban Inna lokacin da ya ke ya jagorantar Sallar idi karama mai Raka’o’i biyu don kawo karshen azumin watan Ramadan na wannan shekarar ta 2026.

A cikin hudubarsa, Imam Baban-Inna ya lura cewa da yawa daga cikin waɗanda suka kammala karatun ba sa samun aikin gwamnati, yana mai kira ga mutane masu hannu da shini da su zuba jari a cikin kamfanoni na halal waɗanda za su iya ɗaukar dumbin matasa aiki kana ya yi bayanin cewa yawan jama’a na buƙatar tsari da ƙwarewa wajen koyo da samar da sana’o’i don dogaro da kai.

Ya shawarci Musulmai da su nemi taimako daga Allah SWT maimakon roƙon mutane kana yayi kira ga masu kuɗi a cikin al’umma da su guji rowa da kuma yin karimci wajen kura da bukatum al’umma don samun rahamar Allah.

Babban Limamin wanda ya bayyana cewa shan miyagun ƙwayoyi ya zama babban matsala a duniya wadda ke haifar da barazana ga al’ummar zamani ta hanyar lalata lafiyaĖr jiki da dai-daita iyalai da kuma ƙarfafa ƙungiyoyin ta’adanci ya shawarci iyaye da su sanya ido kan ‘ya’yansu don kare su.

Ya baiwa Musulmi kwarin gwiwa da su riƙe darussan da suka koya da aiki dashi cikin watan Ramadan don samun yardar Allah SWT .

Wani Mashhurin Malamin Addinin Musulunci a Bauchi Imam Akibu Iliyasu wadda ya nuna gidiyar ga Allahu S.W.T da ya nuna wa musulimi karshen watan Azumin Ramada cikin aminci duk da matsin Tattalin arziki da ake fama da shi, ya yi karin haske ga me da muhimmamci wannan rana ga Musulmi.

A cikin sakonsa, Mai Martaba Sarkin Bauchi, Alhaji Dr. Rilwan Suleiman Adamu, wanda ya yaba wa dukkanin malaman Musulunci da suka gudanar da Tafseerin Alƙur’ani na wannan shekarar cikin lumana, ya yi kira ga Musulmi da su hada kuma kada su yi kasa a gwiwa wajen addu’o’in zaman lafiya da kwanciyar hankali ga kasar nan.

Ana shi bangaren Gwamna Bala Muhammad ya yi kira ga Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci wajen gudanar da addu’o’in zaman lafiya da kawo karshen ta’dacin ga al’ummomin da Gwanna, Digare, Yalo da Mansur duk a karamar hukumar Alkaleri da ayyukan ‘yan ta’adda ya dai dai su

Dubban Musulmai ne dai daga fadin jihar ciki har da Gwamnan da Sarkin Bauchi  da manyan jami’an gwamnati da dattawan garin Bauchi da Malaman Musulunci da shugabannin gargajiya da na al’umma da dai sauransu, suka halarci sallar Idin.

Radiyon Najeriya ya lura cewa bikin wanda aka gudanar karkashin kulawar tsaro na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro da kevfadin jihar ya gudana cikin lumana a dukkan kananan hukumomi ashirin na jihar.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara