Labarai
TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu al’ummomi a Karamar Hukumar Borgu ta jihar, wanda ya yi sanadin salwantar rayuka da dama.
A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamna, Bologi Ibrahim, ya fitar wa manema labarai a Minna, gwamnan ya bayyana harin a matsayin mugun aiki da ta’asa da rashin imani, wanda ya janyo mutuwar mutane da dama, sace wasu, tare da lalata hanyoyin dogaro da rayuwar jama’a.
Gwamna Umar Bago ya miƙa ta’aziyyarsa ta musamman ga al’ummomin da abin ya shafa, musamman waɗanda harin ya rutsa da su da iyalansu a Kasuwar Daji da ƙauyen Sukumbara. Ya bayyana cewa waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Musulmi da Kiristoci daga sassa daban-daban na Karamar Hukumar Borgu a Jihar Neja.
Gwamnan ya ce abin yana da ɗaure kai da tayar da hankali ganin an fara sabuwar shekara da irin wannan mummunan lamari. Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da dogaro ga Allah, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa na haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro domin inganta tsaro a yankunan da abin ya shafa.
A cewarsa, ƙungiyar tsaro ta haɗin gwiwa na bin sawun ‘yan ta’addan da nufin ceto waɗanda aka sace. Ya kuma yi addu’ar Allah Ya jiƙan rayukan waɗanda suka rasu, Ya kubutar da waɗanda aka sace, Ya ba waɗanda suka jikkata lafiya.
A halin da ake ciki kuma, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta bakin Mai Ba Shi Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Bayo Onanuga, ya bayar da umarni ga Sojoji, ‘Yan Sanda da DSS da su farauto ‘yan ta’addan da ke da hannu a harin Kasuwar Daji.
PR Aliyu Lawal
-
Labarai3 days agoGwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah
-
Labarai6 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai6 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai6 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai2 days agoGidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai3 days ago‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa
-
Labarai3 days agoJIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah
