Connect with us

Labarai

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Published

on

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu al’ummomi a Karamar Hukumar Borgu ta jihar, wanda ya yi sanadin salwantar rayuka da dama.

A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamna, Bologi Ibrahim, ya fitar wa manema labarai a Minna, gwamnan ya bayyana harin a matsayin mugun aiki da ta’asa da rashin imani, wanda ya janyo mutuwar mutane da dama, sace wasu, tare da lalata hanyoyin dogaro da rayuwar jama’a.

Gwamna Umar Bago ya miƙa ta’aziyyarsa ta musamman ga al’ummomin da abin ya shafa, musamman waɗanda harin ya rutsa da su da iyalansu a Kasuwar Daji da ƙauyen Sukumbara. Ya bayyana cewa waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Musulmi da Kiristoci daga sassa daban-daban na Karamar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

Gwamnan ya ce abin yana da ɗaure kai da tayar da hankali ganin an fara sabuwar shekara da irin wannan mummunan lamari. Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da dogaro ga Allah, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa na haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro domin inganta tsaro a yankunan da abin ya shafa.

A cewarsa, ƙungiyar tsaro ta haɗin gwiwa na bin sawun ‘yan ta’addan da nufin ceto waɗanda aka sace. Ya kuma yi addu’ar Allah Ya jiƙan rayukan waɗanda suka rasu, Ya kubutar da waɗanda aka sace, Ya ba waɗanda suka jikkata lafiya.

A halin da ake ciki kuma, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta bakin Mai Ba Shi Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Bayo Onanuga, ya bayar da umarni ga Sojoji, ‘Yan Sanda da DSS da su farauto ‘yan ta’addan da ke da hannu a harin Kasuwar Daji.

PR Aliyu Lawal

Labarai

Labarai9 hours ago

Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Juma’a 1 ga Watan Shawwal

Daga Nasir Malali Mai Martaba Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Juma’a, 20 ga watan Maris a matsayin...

Labarai2 days ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai3 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai3 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai3 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai3 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai3 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai6 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Mafi Shahara