Connect with us

Labarai

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Published

on

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru.

Malam Suleiman Lawal, mai shekaru 78, ya rasu a daren Asabar, 3 ga Janairu, 2026, bayan fama da doguwar jinya.

Kafin rasuwarsa, ya kasance Sakataren Kwamitin Aiki da cikawa (Task Force Committee) kan gina Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH), Shika, Zariya, da kuma Cibiyar kula da lafiyar Ido ta Ƙasa (National Eye Center), Kaduna.

A baya, ya riƙe muhimman mukamai da dama, ciki har da shugaban Kwalejin Fasaha ta Jihar Kaduna dake Zariya (wacce yanzu ake kira Nuhu Bamalli Polytechnic, Zariya), Kwamishinan Tarayya a Hukumar kula da da’ar Ma’aikata Federal Character Commission mai wakiltar Jihar Kaduna, da kuma Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, da sauransu.

Marigayi Jarman Kauru ya rasu ya bar mata biyu, ’ya’ya 14, da jikoki da dama.

Daga cikin ’ya’yansa akwai Alhaji Nuraddeen Suleiman Lawal Mayana Kauru, Sakataren Ilimi (Academic Secretary) na kwalejin kimiyya da fasaha ta Nuhu Bamalli, Zariya.

An gudanar da sallar jana’izan sa a Filin Eid na Mallawa da ke Ban Zazzau, Zariya, da misalin karfe 1:30 na rana, Lahadi, 4 ga Janairu, 2026.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa kurakuransa, Ya kuma ba shi Aljannar Firdausi.

Yusuf Zubairu

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara