Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba

Published

on

Daga Khadijah Aliyu 

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta karɓi wasiƙa daga Gwamna Abba Kabir Yusuf kan gabatar da kasafin kuɗi na shekarar 2026 wanda ya kai Naira tiriliyan 1, irinsa na farko a tarihin jihar.

Za a gabatar da kudurin ne a ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamban 2025.

Wasiƙar, wadda Kakakin Majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya karanta a zaman majalisar, ta bayyana cewa gabatar da kasafin ya yi daidai da sashe na 121 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999, wanda aka yi wa gyara.

Gwamna Yusuf ya bayyana cewa yawan kasafin da ya karu sosai na nuna ƙudurin gwamnatinsa na ƙarfafa manyan ayyukan gine-gine, shirye-shiryen sabunta birane, da haɓaka ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a fadin jihar Kano.

Shugaban Majalisar ya ce Gwamna Yusuf ya yi bayanin cewa kasafin na 2026 zai mayar da hankali ne kan raya gidaje, aikin gona, ilimi, kiwon lafiya, da tallafawa ƙanana da matsakaitan sana’o’i, domin farfaɗo da tattalin arziƙi da samar da hanyoyin dogaro da kai ga al’ummar Kano.

Da zarar an gabatar da kudirin, za a miƙa kasafin kuɗin zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano domin nazari da amincewa. Idan aka amince da shi, zai kasance kasafin kuɗi na farko mai irin wannan girma da jiha daga Arewa ta gabatar.

Gwamna Yusuf ya sake tabbatar da aniyarsa ta gaskiya, bin ƙa’ida wajen kashe kuɗi, da tabbatar da cewa kowane bangare ya samu tallafi isasshen da zai ba shi damar samar da ingantattun ayyuka ga jama’ar Kano.

 

Labarai

Labarai10 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi11 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai11 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara