Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Bukaci Asibitin Koyarwa Na RSUTH Ya Bada Fifiko Ga ‘Yan Asalin Jihar

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnatin jihar Jigawa ta yi kira ga hukumar gudanarwar asibitin koyarwa na Rasheed Shekoni da ta ba da kulawa ta musamman ga yan asalin jihar wajen daukar aiki.

Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin da babban likitan asibitin Dr. Salisu Mu’azu Babura da ma’aikatan asibitin suka kai masa ziyarar a gidan gwamnati dake Dutse.

Malam Umar Namadi ya bayyana cewar jihar Jigawa tana da kwararru da kuma masana da za su iya cike gibin guraben ayyukan lafiya a asibitin na Rasheed Shekoni.

Gwamnan ya kuma bada tabbacin ci gaba da tallafawa asibitin don cimma nasarorin da aka sanya a gaba.

Malam Umar Namadi ya kuma bayyana cewar gwamnatin jihar za ta kari fili domin yin karin gine gine a asibitin.

Tunda farko a nasa jawabin, Babban likitan asibitin Dr. Salisu Mu’azu Babura yace sun kai ziyarar ce domin gabatar da kansu da kuma neman karin hadin kai da goyan bayan gwamnatin jihar wajen ci gaban asibitin.

Dr. Salisu Babura ya shedawa Gwamnan ma’aikatan asibitin da gwamnatin tarayya ke biyan albashi sun kai 877.

Ya kuma yi nuni da cewar cikin adadin, guda 250 sun fito ne daga jihar jigawa.

Kazalika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyan bayan da ke baiwa asibitin.

Yana mai fatan kara bullo da wasu hanyoyi domin magance kalubalen da ke fuskantar asibitin a yanzu.

 

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara