Connect with us

Labarai

Mazauna Sabon Gero Sun Koka Kan Watsi Da Aikin Gyaran Hanyarsu

Published

on

 

Mazauna unguwar Sabon Gero, dake bayan Millennium City a Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, sun roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta kammala aikin gyaran titin unguwar, wanda suka ce an bar shi a cikin mawuyacin hali duk da cewa an bai wa wani kamfani aikin kusan shekara guda da ta gabata.

 

Mazauna yankin sun bayyana cewa halin da hanyar take ciki ya jefa su cikin matsanancin rayuwa, musamman mata masu juna biyu da ke tilasta musu hawa babura domin neman kulawa a wajen unguwar, kasancewar babu asibiti a yankin.

 

Ɗaya daga cikin mazauna, Rashida Shehu, wadda ke da juna biyu, ta ce ta ji rauni a lokacin da take kokarin bin hanyar zuwa gari domin kula da lafiya, inda ta roƙi gwamnati ta taimaka musu cikin gaggawa.

 

Haka kuma, rashin makarantar gwamnati a Sabon Gero ya sanya yaran mazauna yankin cikin wahala, saboda da dama daga cikinsu ba sa iya jure tafiyar neman ilimi zuwa waje.

 

Manoma kuma sun koka kan yadda rashin titin ke hana su kai kayayyakin gona kasuwa.

 

Mai unguwar Sabon Gero, Mai Anguwa Sunusi, ya bayyana cewa tun shekara guda da ta gabata aka bai wa kamfanin gyaran hanya na Think Lab aikin, amma har yanzu babu wani ci gaba da aka gani a wajen.

 

Ya roƙi gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da ya sanya wa aikin titin muhimmanci don amfanin al’umma da jihar baki ɗaya.

A nasa bangaren, matasa ƙarƙashin kungiyar cigaban Sabon Gero sun yi barazanar gudanar da zanga-zangar lumana idan aka ci gaba da yin shiru kan aikin, inda suka ce jinkirin kammalawa ya jawo tsaikon ci gaba tare da jefa al’umma cikin haɗari da matsalolin tsaro.

 

’Yan kasuwa da masu sana’o’i a yankin sun kuma ce lalacewar titin ta rage masu ciniki, tare da hana masu saka jari daga wajen zuwa yin kasuwanci a Sabon Gero.

 

A cewar su, wannan yanayi ya sabawa alkawuran gwamnati na samar da ci gaban kowa da kowa, abin da ya sa suke jin an nuna musu wariya.

 

COV: Khadija Kubau

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara