Connect with us

Labarai

Hisbah Ta Kama Wani Mutum Da Ke Yunkurin Safarar Mata 12 A Kano

Published

on

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wani mutum da ake zargi da safarar mutane tare da mata 12 a wata tashar mora da ke kan titin  Zaria.

Rahotanni sun bayyana cewa mutumin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an kama shi ne  yana yunkurin safarar matan  zuwa Legas.

Mataimakin Kwamandan Janar na Hisbah, Sheikh Mujahideen Aminuddeen, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa, inda ya ce jami’an hukumar karkashin jagorancin jami’in da ke kula da tashoshin mota, Muhammad Bashir ne suka cafke wanda ake zargin, wanda dan asalin jihar Borno ne.

Bincike na farko ya nuna cewa an shirya safarar matan ne zuwa kasashen waje ta hanyar Legas, inda za su bi ta Jamhuriyar Benin da kumGhana, sannan daga bisani a kaisu Saliyo.

Ana zargin wanda aka kama da tsara musu takardun izinin shiga kasar Saudiyya domin neman aikin yi.

A cewar Hisbah, matan sun bayyana yayin bincike cewa kowannensu ta riga ta biya Naira miliyan ɗaya da rabi (₦1.5m) a matsayin kafin alkalami, tare da yarjejeniyar cewa za su biya sauran kudin bayan sun samu ayyukan yi a ƙasar da za a kaisu.

Hukumar ta nuna damuwa cewa irin wannan kudi mai yawa na iya zama jari domin dogaro da kai a gida.

Aminuddeen ya ce matan sun bambanta a shekaru, ciki har da wadda ta kai shekara 50, wasu biyu ’yan shekara 23, wasu biyu kuma ’yan shekara 20, yayin da sauran mafi yawan su ’yan shekara 15 ne kacal. Sun fito ne daga jihohin Katsina, Kano, Borno, Jigawa da Zamfara.

Wannan abin takaici ne,” in ji shi. “Kudin da suka biya ya isa su fara sana’a mai kyau a jiharsu. Amma suka zabi su sa kansu cikin hadarin irin wannan tafiya.” Ya bukaci iyaye da su ja hankalin ’yayansu game da irin waɗannan lamurra masu hadari.

Kwamandan ya gargadi cewa ko da sun samu takardar izinin shiga Saudiyya, babu tabbacin aikin da za su yi a can. “Idan kuma an kasa samun visa, za a karkatar da su zuwa Saliyo. Wannan lamari hadari ne kuma abin takaici,” In ji shi.

Daga karshe, hukumar Hisbah ta mika wanda ake zargi da matan ga Hukumar Yaki da Safarar Mutane ta Kasa (NAPTIP) domin gudanar da cikakken bincike da daukar matakan da suka dace.

 

Daga Khadijah Aliyu 

 

 

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara