Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoma 352 A Nasarawa Da Kayayyakin Noma Na Zamani

Published

on

Gwamnatin Tarayya tare da Asusun Samar da Kudade Domin Bunkasa Harkokin Noma(IFAD) da Shirin Sarrafa Amfanin Gona (VCDP) sun fara raba kayayyakin noman zamani da mashin mai kafa uku  ga manoma 352 a Jihar Nasarawa domin kakar noman bana.

Shugabar shirin IFAD-VCDP, Dr. Eunice Adgidzi ce ta kaddamar da rabon kayayyakin a Lafiya, babban birnin jihar, inda ta ta bayyana cewa shirin ya fi karkata ne ga kanana manoman shinkafa da rogo.

Ta ce shirin wani bangare ne na ƙoƙarin da ake yi na sauya fannin noma zuwa abin da zai kawo wadatar abinci, samar da arziki da kuma ci gaba mai ɗorewa a Jihar Nasarawa.

Manoma 352 da suka amfana an zaɓo su ne daga kananan hukumomi biyar da shirin ya shafa a jihar, da suka hada da Lafiya, Nasarawa, Doma, Karu da Wamba.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhunan iri shinkafa mai  nauyin kilo 9,600, da buhunan 1,408 takin NPK 1,408, da buhuna 384 na takin Urea, da lita 352 na maganin ciyawa mara zaɓi, da lita 352 na maganin ciyawa mai zaɓi, da kuma rassa 8,000 na rogo domin dashe.

Haka kuma, an raba mashin mai kafa uku guda tara ga wasu manoma domin sauƙaƙe musu jigilar kayan gona zuwa kasuwa, wanda hakan zai taimaka wajen rage asarar bayan girbi.

Dr. Adgidzi ta jaddada cewa haɗin gwiwar Gwamnatin Tarayya da IFAD da gwamnatin jihar, na nuna jajircewar samar wa manoma kayan aikin da za su taimaka musu wajen samun nasara.

A nasa jawabin, Kwamishinan Noma na Jihar Nasarawa, Alhaji Umaru Tanko Tunga, ya bayyana cewa wannan shiri zai ƙara samar da abinci, rage asarar bayan girbi da kuma inganta rayuwar kananan manoma.

Ya shawarci manoman da suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya kamata, sannan ya yaba wa Gwamna Abdullahi Sule bisa samar da yanayin da ya ba da damar nasarar shirye-shiryen noman a jihar.

A martanin su, wasu daga cikin manoman da suka amfana kamar su Lazarus Okwugya daga Assakio, da Joseph Abimiku da Fatima Shuaibu daga unguwar Azuba, sun nuna godiya ga shirin VCDP bisa irin tallafin da ya kawo, wanda suka ce ya inganta yawan amfanin gona da kuma rayuwarsu.

 

Daga Aliyu Muraki

 

 

Labarai

Labarai13 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi14 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai14 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai16 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara