Connect with us

Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki Da Dama A Karamar Hukumar Bodinga

Published

on

Daruruwan iyalai da manoma sun shiga cikin muwuyacin hali  sakamakon iftila’in ambaliya da ta afka a kauyen Badau da ke gundumar Darhela da Butuku a gundumar Toma, ƙaramar hukumar Bodinga a jihar Sakkwato.

Ambaliyar ta nutse da dubban gonaki, ta rusa gidaje, tare da lalata kasuwar garin Dandin-Mahe da ke cikin ƙaramar hukumar Shagari, abin da ya jefa al’ummar yankin cikin tashin hankali.

A cewar rahoton farko, sama da gonaki 3,000 ne suka lalace a Badau, yayin da gonaki 75 suka lalace a Butuku.

Bisa ga rahoton hukumar ƙaramar hukumar Bodinga, tawagar haɗin gwiwa daga Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Sakkwato (SEMA) da Hukumar Kula da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ofishin Sakkwato, sun kai ziyara yankunan da lamarin ya shafa domin tantance irin asarar da aka yi.

Jagoran tawagar shi ne Daraktan Tallafi da Sake Gina Rayuwa na SEMA, Malam Mustapha Umar, tare da jami’in tsare-tsare na NEMA a Sakkwato, Mista Tukur Abubakar.

Rediyon Najeriya a Sakkwato ya ruwaito cewa iftila’in ya biyo bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka kwashe kwanaki huɗu ana yi lokaci zuwa lokaci a yankin.

Mazauna yankin sun roƙi gwamnatin jiha da ta tarayya da su kawo tallafin gaggawa domin rage musu ƙuncin da suke ciki.

Tawagar SEMA da NEMA sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za su tattara bayanan da suka tara domin gabatar wa ga hukumomi don hanzarta kawo agajin gaggawa.

Tawagar ta kuma kai ziyara wasu yankuna a cikin ƙaramar hukumar Shagari inda ambaliyar ta shafi ƙauyuka huɗu, tare da lalata kasuwa da gonaki 74, da kuma jawo asarar gine-gine.

Har ila yau, wani gida ya rushe sakamakon ambaliyar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar yaro mai shekaru bakwai mai suna Jafar Sani.

 

Daga Nasiru Malali

 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara