Ilimi
Daliban Makarantar Kuriga Sun Shaki Iskar ‘Yanci – Uba Sani
Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sakin yara ‘yan makaranta dari biyu da tamanin da bakwai 287 da aka yi garkuwa da su daga Kuriga da ke karamar hukumar Chikun ta jihar
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan jihar Uba Sani.
Sanarwar ta ce “Ina so in sanar da cewa an sako yaranmu na makarantar Kuriga, muna godiya ta musamman ga mai girma shugaban mu, Bola Ahmed Tinubu, bisa ba da fifiko ga tsaro da tsaron ‘yan Nijeriya, musamman kokarin da ya yi na ganin an sako ‘ya’yan makarantar Kuriga da aka sace ba tare da wani lamuni ba”.
Gwamnan ya kuma yaba da jajircewar hafsoshin sojojin Najeriya na ganin an samu nasarar sako yaran.
“Muna kuma gode wa daukacin ‘yan Najeriya bisa addu’in da suka yi na ganin Allah Ya dawo da yaran cikin koshin lafiya, lallai wannan ranar farin ciki ce. Muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki.”
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 7 ga watan Maris, 2024, ‘yan bindiga suka sace ‘yan makarantar firamare da na Sakandaren Gwamnati da ke Kuriga, inda suka kai su dajin.
Masu garkuwa da mutanen sun bukaci a bada kudin fansa na Nera milyan dubu daya, yayin da suka ba da wa’adin ranar 27 ga Maris, 2024, don biyan kudin.
Aminu Dalhatu
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai17 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai17 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati