Connect with us

Ilimi

An Bukaci Masu Hannu Da Shuni Su Rika Taimakawa Marasa Galihu a Watan Ramadan

Published

on

An bukaci masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa karfi dake cikin al’umma domin su gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Adamu Ubaidullah ya yi kiran lokacin da ya zanta da wakilin Radio Najeriya a zaria.

Ya bayyana cewa idan aka yi la’akari da matsin tattalin arzikin kasa ke fuskanta ya zama wajibi al’umma su rungumi dabi’an taimaka wa junan su, musamman a wannan wata na azumin watan Ramadan.

Marafan Yamman na Zazzau ya ce akwai dimbin laba ga duk mutumin da ya ciyar da wani a wannan lokaci, musamman ganin yadda kayan masarufi ya yi tsada ta yadda mutane da dama basa iya ciyar da iyalan su.

Alhaji Adamu Ubaidullahi ya kuma shawarci jama’a da su yi amfani da wannan watan mai albarka wajen yin addu’o’in Allah ya kawo wa kasar nan mafita,musamman ta fuskar rashin tsaro da kuma magance talauci.

Ya kuma bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su maida hankali wajen taimakawa kananan manoma domin su iya gudanar da mona idan damina ta fadi.

Ubaidullahi ya bayyana cewa dole sai gwamnati ta tallafawa manoma kasancewar kayan aikin noma ya yi matukar tsada ga kuma rashin ratso dake neman hana yin noman.

Ya kara da cewa kamata ya yi gwamnati ta sa hannun sarakunan gargajiya yayin taimaka wa manoman kasancewar sune suka san manoman gaskiya ba manoman biro ba.

Marafan Yamman Zazzau ya yaba wa maimartaba sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa jajircewar da ya yi na samar da sauye-sauye domin ciyar da masarautar Zazzau gaba.

A don haka sai ya bukaci al’ummar masarautar Zazzau da su gaba da baiwa maimarta sarkin na Zazzau goyon baya da hadin kai domin ya sami karin karfin gwiwar samar da alhairai ga masarautar.

INT/HALIRU HAMZA

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai16 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai17 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara