Ilimi
An Bukaci Masu Hannu Da Shuni Su Rika Taimakawa Marasa Galihu a Watan Ramadan
An bukaci masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa karfi dake cikin al’umma domin su gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.
Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Adamu Ubaidullah ya yi kiran lokacin da ya zanta da wakilin Radio Najeriya a zaria.
Ya bayyana cewa idan aka yi la’akari da matsin tattalin arzikin kasa ke fuskanta ya zama wajibi al’umma su rungumi dabi’an taimaka wa junan su, musamman a wannan wata na azumin watan Ramadan.
Marafan Yamman na Zazzau ya ce akwai dimbin laba ga duk mutumin da ya ciyar da wani a wannan lokaci, musamman ganin yadda kayan masarufi ya yi tsada ta yadda mutane da dama basa iya ciyar da iyalan su.
Alhaji Adamu Ubaidullahi ya kuma shawarci jama’a da su yi amfani da wannan watan mai albarka wajen yin addu’o’in Allah ya kawo wa kasar nan mafita,musamman ta fuskar rashin tsaro da kuma magance talauci.
Ya kuma bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su maida hankali wajen taimakawa kananan manoma domin su iya gudanar da mona idan damina ta fadi.
Ubaidullahi ya bayyana cewa dole sai gwamnati ta tallafawa manoma kasancewar kayan aikin noma ya yi matukar tsada ga kuma rashin ratso dake neman hana yin noman.
Ya kara da cewa kamata ya yi gwamnati ta sa hannun sarakunan gargajiya yayin taimaka wa manoman kasancewar sune suka san manoman gaskiya ba manoman biro ba.
Marafan Yamman Zazzau ya yaba wa maimartaba sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa jajircewar da ya yi na samar da sauye-sauye domin ciyar da masarautar Zazzau gaba.
A don haka sai ya bukaci al’ummar masarautar Zazzau da su gaba da baiwa maimarta sarkin na Zazzau goyon baya da hadin kai domin ya sami karin karfin gwiwar samar da alhairai ga masarautar.
INT/HALIRU HAMZA
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai17 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai16 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet