Ilimi
An Bukaci Masu Hannu Da Shuni Su Rika Taimakawa Marasa Galihu a Watan Ramadan

An bukaci masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa karfi dake cikin al’umma domin su gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.
Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Adamu Ubaidullah ya yi kiran lokacin da ya zanta da wakilin Radio Najeriya a zaria.
Ya bayyana cewa idan aka yi la’akari da matsin tattalin arzikin kasa ke fuskanta ya zama wajibi al’umma su rungumi dabi’an taimaka wa junan su, musamman a wannan wata na azumin watan Ramadan.
Marafan Yamman na Zazzau ya ce akwai dimbin laba ga duk mutumin da ya ciyar da wani a wannan lokaci, musamman ganin yadda kayan masarufi ya yi tsada ta yadda mutane da dama basa iya ciyar da iyalan su.
Alhaji Adamu Ubaidullahi ya kuma shawarci jama’a da su yi amfani da wannan watan mai albarka wajen yin addu’o’in Allah ya kawo wa kasar nan mafita,musamman ta fuskar rashin tsaro da kuma magance talauci.
Ya kuma bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su maida hankali wajen taimakawa kananan manoma domin su iya gudanar da mona idan damina ta fadi.
Ubaidullahi ya bayyana cewa dole sai gwamnati ta tallafawa manoma kasancewar kayan aikin noma ya yi matukar tsada ga kuma rashin ratso dake neman hana yin noman.
Ya kara da cewa kamata ya yi gwamnati ta sa hannun sarakunan gargajiya yayin taimaka wa manoman kasancewar sune suka san manoman gaskiya ba manoman biro ba.
Marafan Yamman Zazzau ya yaba wa maimartaba sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa jajircewar da ya yi na samar da sauye-sauye domin ciyar da masarautar Zazzau gaba.
A don haka sai ya bukaci al’ummar masarautar Zazzau da su gaba da baiwa maimarta sarkin na Zazzau goyon baya da hadin kai domin ya sami karin karfin gwiwar samar da alhairai ga masarautar.
INT/HALIRU HAMZA
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
