Connect with us

Labarai

Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hada kai da ayyukan tsaro a Jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, kamar yadda babi na biyu na kundin tsarin mulki ya tanada.

 

A zaman taron na ranar Talata, mambobin sun yi zargin cewa, ‘yan bindiga sun mamaye al’ummomi da dama a fadin jihar Zamfara, kuma sun zargi Gwamnan da mayar da hankali kan burin siyasa da kuma zargin abokan hamayya.

 

Sun kuma yi zargin cewa, Gwamnan bai kai ziyara ko aika tallafi ga al’ummomin da hare-hare ya shafa ba, inda suka ce ziyarar da ya shirya kai wa al’ummar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda ta kasance da alaka da siyasa gabanin zaben fidda gwani na majalisar dokokin jihar.

 

A nasa gudunmuwar, Bashir Abubakar Masama na Bukkuyum ta Arewa ya yabawa kokarin gwamnatin tarayya na yaki da ‘yan fashi, inda ya bayyana cewa Adapka, Zauma, Gwashi, da Mayanchi a mazabarsa sun sha fama da hare-hare akai-akai.

 

Da yake goyon bayan kudirin, Bashir Bello Sarkin Zango na Bungudu ta Yamma, ya yi zargin cewa, Gidan Bugaje, Zaman Gida, Kukan Tara, da Gidan Dan-Inna, gungun miyagu sun mayar da yankin nasu, yayin da shugaban marasa rinjaye Aliyu Ango Kagara na Talata Mafara ta Kudu ya sanya Morai, Bobbo, Makera, Jangebe, Gwaram, da Ruwan Gizo a matsayin kauyukan da lamarin ya fi shafa a mazabarsa.

 

‘Yan majalisar sun bukaci gwamnatin tarayya da ta yi watsi da gwamnatin jihar a harkokin tsaro.

 

Sun yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.

 

A nasa bangaren, Ibrahim Tudu Tukur na Bakura ya yi zargin cewa al’ummarsa na ci gaba da zama a killace da ‘yan bindiga, inda ya bayar da misali da harin da aka kai a kwanan nan a Damri, Dakko, Sama, Sabon Garin Damri, da Sade, yayin da Faruk Musa Dosara na Maradun ya yi kira da a duba yiwuwar tsige Gwamnan bisa zarginsa da yin sakaci da aikinsa.

 

Ya kuma jaddada bukatar mazauna yankin su baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai kan duk wani nau’in da ake zargi da aikata laifuka domin a kama su kafin su aikata wani laifi.

 

Sun kuma yi alkawarin ci gaba da yin kira da a samar da shugabanci na gari a Zamfara domin ci gaban jihar.

 

AMINU DALHATU.

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara