Connect with us

Labarai

Dokar Auren Jinsi: Majalisar Ghana Ta Fusata Da Matakin Nana Akufo Addo

Published

on

Kakakin Majalisar Ghana ya ki amincewa da sahale nadin wasu sabbin ministoci bisa kafa hujja da cewa har sai shugaban kasar Nana Akufo-Addo ya sanya hannu a dokar haramta auren jinsi da Majalisar ta kada kuri’ar amincewa da ita a watan jiya, amma har zuwa yanzu shugaban ya gaza sanya hannu.

Ana dai ganin shugaba Nana Akufo-Addo na jan kafa wajen rattaba hannu kan kudirin don mayar da shi doka ne sakamakon kakkausar sukar da kudirin ke fuskanta daga kungiyoyin kare hakkin dan adam musamman daga kasashen Turai.

 

Kafin wannan mataki na Majalisar dai, shugaba Addo ya ce yana jiran hukuncin kotun kolin kasar gabanin rattaba hannu kan dokar, bayan da masu fafutukar tabbatar da auren na jinsi suka daukaka kara kan matakin.

 

Wasu alkaluma da aka tattara na nuna cewa galibin al’ummar Ghana na goyon bayan haramta auren na jinsi da kuma tanadin hukunci mai tsauri kan wadanda aka samu da aikatawa ko kuma da goyon baya koma tallata shi.

 

Sai dai wasu bayanai na cewa, shugaba Akufo-Addo ya samu gargadi ne daga kasashen duniya da hukumomin bayar da lamuni da ke neman lallai kar ya sanya hannu a kudirin don mayar da shi dokar.

Ghana dai ba ita ce kasar farko da ke fuskantar matsala wajen aiwatar da wannan doka ta haramta auren jinsi ba, domin kuwa makamancin lamarin da ke faruwa a Kenya kenan, inda har zuwa yanzu kungiyoyin addinai ke ci gaba da gangami don kalubalantar mahukunta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai4 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara