Connect with us

Labarai

Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa ya Samu Gagarumar Nasara a Karamar Hukumar Gwarzo

Published

on

Shirin Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa (MNCH) a Karamar Hukumar Gwarzo ta Jihar Kano ya samu gagarumar nasara, inda mata da yara da dama suka amfana da ayyukan kiwon lafiya kyauta iri-iri.

Wannan kamfen na mako guda, wanda Gwamnatin Jihar Kano tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa suka tallafa masa, na da nufin inganta lafiyar mata da yara tare da rage mace-macen da za a iya kauce wa ta hanyar samar da dama ga ayyukan kiwon lafiya.

Cibiyoyin lafiya a fadin karamar hukumar, ciki har da Asibitin Gwamnati na Gwarzo da Asibitin ‘Yar Kasuwa, sun bayar da rigakafi kyauta, shawarwari kan abinci mai gina jiki, kulawar haihuwa da sauran muhimman ayyuka na kiwon lafiya.

Jami’in Lafiya a matakin farko na karamar hukumar Gwarzo, Alhaji Sulaiman Abdulqadir Karaye, ya bayyana cewa gwamnatin jiha ta tabbatar da samuwar ingantattun magunguna da kayan aiki.

Ya shawarci mata da masu kula da yara su rika amfana da irin waɗannan damar ta hanyar ziyartar cibiyar kiwon lafiya mafi kusa domin samun ayyuka kyauta.

Gwamnatin Kano ta bai wa fannin kiwon lafiya muhimmanci ta hanyar tallafi na baya-bayan nan da suka haɗa da na’urar sanyaya allurar rigakafi, janareto da sauran kayan aiki masu muhimmanci,” in ji shi.

Shugaban Asibitin ‘Yar Kasuwa kuma wakilin al’umma a Gwarzo, Salisu Ibrahim, ya bayyana jin daɗinsa kan yawan halartar jama’a.

Ya ce mazauna yankin sun fito sosai domin amfana da ayyukan da aka tanada.

A nata jawabin, jami’ar da ke kula da shirye-shiryen MNCH a karamar hukumar, Hajiya Amina Ado, ta bayyana cewa an gudanar da shirin lafiya cikin nasara a manyan cibiyoyin lafiya tare da wadatattun ma’aikata da kayan aiki.

Ta tabbatar da cewa mata da dama sun halarta, kuma ta yabawa haɗin gwiwar da ke tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ɗaya daga cikin masu amfana a Asibitin ‘Yar Kasuwa, Shamsiyya Abubakar, ta yaba wa gwamnatin jiha da ta ƙaramar hukuma bisa samar da magunguna kyauta, inda ta bayyana shirin a matsayin ceton rai ga mata da dama a yankin.

Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa a Jihar Kano na da nufin kai ayyukan lafiya zuwa yankunan da ke da karancin samun kulawa, tare da rage gibin da ke tsakanin mata da yara wajen samun ingantacciyar kulawa.

 

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara