Connect with us

Labarai

Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki

Published

on

Wata kungiya mai zaman kanta mai suna Kukah Centre ta ce ta kuduri aniyar horar da jami’an tsaro a jihohin Sokoto, Kaduna da Benue.

 

Daraktan Cibiyar Kukah Reverend Father Atta Barkindo, wanda ya bayyana hakan ya ce an dauki matakin ne domin taimakawa kokarin gwamnatin tarayya wajen magance matsalolin tsaro da ke ci gaba da addabar al’ummar kasar.

 

Reverend Father Atta Barkindo, ya jaddada cewa an shirya horon ne domin inganta tsaro a tsakanin al’umma a cikin dimbin kalubalen da jihohi da dama ke fama da su a fadin kasar nan.

 

Ya kuma bayyana bukatar kafa jami’an tsaro na Jihohi su samar da ingantattun tsare-tsare don tabbatar da samar da ayyuka masu inganci.

 

Shima da yake jawabi, jami’in kula da ayyukan cibiyar Kukah, Terseer Bamber, ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin jami’an tsaron jihar sun fuskanci tuhume-tuhume na take hakkin dan Adam da cin zarafin mata.

 

Ya jaddada mahimmancin magance wadannan matsalolin a matsayin wani abin da ake bukata domin samun ci gaba mai dorewa a Najeriya.

 

Ana aiwatar da aikin horon ne tare da haɗin gwiwar Cibiyar Kukah, Ci gaban Ƙasashen Duniya na Birtaniya, da Tetra Tech International Development.

 

A nasa jawabin, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar wanda Sarkin Yakin Gagi, Hakimin Gagi Alhaji Sani Umar Jabbi ya wakilta, ya yi maraba da shirin inda ya bayyana cewa Sarkin Musulmi a shirye yake ya tallafa wa duk wani kokari da zai taimaka kai tsaye wajen samar da zaman lafiya da ci gaban kasa.

 

 

Ya bukaci gwamnatocin jihohi da su ba da fifiko wajen wanzar da zaman lafiya da hadin kai, yana mai korafin cewa kalubalen tsaro ya yi matukar tasiri ga zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasar.

 

Rediyon Najeriya ya rawaito cewa taron ya samu halartar wakilai daga jami’an ‘yan sanda, da Civil Defence, masu aikin shari’a, ‘yan majalisar dokoki, da kuma shugabannin gargajiya, inda ya bayyana tsarin hadin gwiwa na inganta tsaro a Najeriya.

 

Nasir Malali/Sakkwato

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara