Connect with us

Ilimi

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

Published

on

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu a Karamar Hukumar Kaduna Sout

Shirin Dawo da Yara Makaranta na Gwamnatin Jihar Kaduna Mai suna ROOSC ya kaddamar da rabon kayan koyon karatu ga dalibai a Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Jihar Kaduna.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Makarantar Firamare ta LEA da ke Unguwar Mu’azu, inda manyan masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi, musamman shugabannin addini da na al’umma, suka halarta.

Da yake jawabi a wajen taron, Ko’odinetan ROOSC a Jihar Kaduna, Mr. Ezra Angai, ya bayyana cewa wannan shiri hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna da abokan ci gaba da kuma kungiyoyin aiwatar da shirin, domin inganta samun ilimi mai nagarta ga yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya bayyana cewa, ana aiwatar da shirin ne karkashin kulawar Ma’aikatar Ilimi ta jihar tare da hadin gwiwar kungiyoyin Save the Children da UNICEF.

“An samu kudade daga bashin sauki da tallafin da Bankin Raya Kasashen Musulmi (Islamic Development Bank) ya bayar domin aiwatar da wannan shiri,” in ji shi.

Mr. Angai ya ce, Gwamnatin Jihar Kaduna ta samu bashin sauki da tallafi domin magance matsalar yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin jihar.

Ya kara da cewa, shirin zai gina sabbin makarantu guda 102 tare da gyara wasu 170 da ke aiki a yanzu, inda ake sa ran samun kimanin yara 200,000 da ba sa zuwa makaranta a kan gaba a cikin shekara hudu a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

Shi ma da yake jawabi, Jagoran Save the Children a jihar, Malam Tanko Mohammed Langaya, ya bayyana cewa shirin ROOSC yana da kudurin raba kayan koyon karatu da koyarwa sama da 500,000 ga dalibai a makarantu a matsayin wani muhimmin bangare na aiwatar da shirin.

“Wadannan kayan karatu ba wai na kari ba ne kawai, su ne tushen ilimi mai nagarta. Tabbatar da cewa kowane yaro yana da kayan karatu masu dacewa da shekarunsa da al’adarsa da kuma masu jan hankali, muhimmin mataki ne wajen samar da ingantaccen daidaito da ilimi ga kowa da kowa a Jihar Kaduna.”

Ko’odinetan shirin daga Save the Children, Mr. Emmanuel Mbursa, ya jaddada muhimmancin raba kayan karatu guda 100,000, yana mai cewa hakan babbar nasara ce a kokarin dawo da yaran da suka daina zuwa makaranta cikin tsarin ilimin gargajiya.

Ya kuma bayyana bukatar samun goyon bayan al’umma domin dorewar shirin.

A nasa jawabin, Daraktan Tsare-tsare a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Mista Salisu Bala, ya ce shirin na ROOSC yana da nufin bai wa yara ‘yan shekaru 6 zuwa 11 da matasa ‘yan shekaru 12 zuwa 18 da ke wajen makaranta damar samun ilimin firamare mai inganci.

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Gudanar da Makarantun Firamare SBMC na Kaduna South, Alhaji Usman Sani, wanda kuma shi ne Hakimin Badikko, ya jaddada rawar da ilimi ke takawa wajen magance matsalolin rashin tsaro da matsin tattalin arziki a kasar.

Ya bukaci iyaye da shugabannin al’umma da su tabbatar cewa dukkan yara masu shekaru na zuwa makaranta suna halartar makaranta, yana mai bayyana damuwa kan rashin isasshen samun ilimin yara kanana a wasu yankunan jihar.

Alhaji Usman Sani ya yabawa Gwamna Uba Sani bisa kudurinsa na samar da ilimi ga kowa da kowa, yana mai cewa shirin ROOSC wata babbar hanya ce ta tabbatar da ingantacciyar makoma ga yaran Jihar Kaduna.

A halin yanzu, kananan hukumomi tara aka riga aka zaba domin rabon kayan koyon karatu. Sun hada da: Kaduna South, Igabi, Kaduna North, Sabon Gari, Soba da Lere.

Sauran sune: Kachia da Jema’a da kuma Kauru.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara