Connect with us

Kasuwanci

Hukumar Kwastam Shiyar Jihar Kebbi Ta Sake Bude Kan Iyakar Najeriya Da Nijar

Published

on

 

Sabon Shugaban Hukumar Kwastam a Jihar Kebbi, Kwanturola Iheanacho Ernest Ojike, ya bi umarnin Shugaban Hukumar na kasa Bashir Adewale Adeniyi, na sake bude kan iyakar Kamba don ci gaba da hada-hadar kasuwanci a kasashen duniya.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Mohammed Tajuddeen Salisu ya fitar, ya ce Kamba babbar kan iyaka ce mai matukar mahimmanci, da ke samar da kudaden shiga a jihar Kebbi.

Sanarwar ta bayyana cewa, sake bude kan iyakokin zai kara fadada kasuwanci ta halastacciyar hanya da za su yi tasiri wajen gina kasa da inganta tattalin arziki, yana mai cewa hakan ba ya nufin cewa za a yi sakaci ta yadda wasu za su yi amfani da wannan damar wajen shigo da haramtattun kayayyaki da za su yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da kuma kawo cikas ga tsaron kasa ba.

Kwanturolan na jihar ya ce, jami’an hukumar a shirye suke don yin aiki bisa tsarin doka domin saukaka kasuwanci a kan iyakar Kamba ba tare da wata matsala ba, muddin ‘yan kasuwa sun shigo da halastattun kayayyaki da kuma biyan kudaden da suka dace ga asusun Gwamnatin Tarayya.

Sanarwar ta bayyana cewa, Kwanturola Ernest Ojike yana mai jaddada cewa, har yanzu an haramta fitar da kayan abinci zuwa kasashen waje, bisa la’akari da karancin abinci a kasar.

 

Abdullahi Tukur 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai19 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai20 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara