Kasuwanci
Hukumar Kwastam Shiyar Jihar Kebbi Ta Sake Bude Kan Iyakar Najeriya Da Nijar
Sabon Shugaban Hukumar Kwastam a Jihar Kebbi, Kwanturola Iheanacho Ernest Ojike, ya bi umarnin Shugaban Hukumar na kasa Bashir Adewale Adeniyi, na sake bude kan iyakar Kamba don ci gaba da hada-hadar kasuwanci a kasashen duniya.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Mohammed Tajuddeen Salisu ya fitar, ya ce Kamba babbar kan iyaka ce mai matukar mahimmanci, da ke samar da kudaden shiga a jihar Kebbi.
Sanarwar ta bayyana cewa, sake bude kan iyakokin zai kara fadada kasuwanci ta halastacciyar hanya da za su yi tasiri wajen gina kasa da inganta tattalin arziki, yana mai cewa hakan ba ya nufin cewa za a yi sakaci ta yadda wasu za su yi amfani da wannan damar wajen shigo da haramtattun kayayyaki da za su yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da kuma kawo cikas ga tsaron kasa ba.
Kwanturolan na jihar ya ce, jami’an hukumar a shirye suke don yin aiki bisa tsarin doka domin saukaka kasuwanci a kan iyakar Kamba ba tare da wata matsala ba, muddin ‘yan kasuwa sun shigo da halastattun kayayyaki da kuma biyan kudaden da suka dace ga asusun Gwamnatin Tarayya.
Sanarwar ta bayyana cewa, Kwanturola Ernest Ojike yana mai jaddada cewa, har yanzu an haramta fitar da kayan abinci zuwa kasashen waje, bisa la’akari da karancin abinci a kasar.
Abdullahi Tukur
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai20 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai19 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati