Connect with us

Fasaha

Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai

Published

on

Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.

 

Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.

 

Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.

 

A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.

 

“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.

 

 

“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.

 

“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.

 

“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.

 

“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara