Connect with us

Labarai

Ku Karanta Jerin Kamen Da Hukumar NDLEA Ta Yi A Farkon Watan Maris

Published

on

Jami’an Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa NDLEA reshen Jihar Borno, sun kama wasu dattawa biyu kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Hukumar ta bayyana cewa, daga cikin ababen zargin da suka shiga hannu akwai dattijo mai shekara 70 da kuma mai shekara 65.

Femi Babafemi, Daraktan yada labarai da bayar da shawarwari na NDLEA ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Ya ce, an kama wadanda ake zargin ne ranar Asabar 9 ga watan Maris tare da waɗanau matasa biyu — mai shekaru 24 da kuma mai shekaru 28 — a Maiduguri da Gamboru-Ngala.

A ranar Asabar ɗin kuma, jami’an NDLEA a Karamar Hukumar Geidam da ke Jihar Yobe, sun tare wata mota kirar Golf 3 da ke kan hanyar zuwa Gagamari a Jamhuriyar Nijar, inda aka kama wani matashi mai shekaru 28 zai kai tabar wiwi mai nauyin kilogiram 24.5 ga wani dila.

Hakazalika, hukumar ta ce a ranar Talata 5 ga watan Maris, ta kwace kwali 42 mai ɗauke da kwalabe 8,400 na maganin mura mai sa maye, da ke da nauyin kilogiram 1,260 a hannun wani direba mai shekaru 29 a hanyar Katsina.

Kakakin hukumar ya bayyana cewa, sun yi nasarar damke wani dilan haramtattun ƙwayoyin da ya ɓoye kayan mayen a injin wata motar bas.

Ya ce “Sun kama wani da wiwi da ta kai kilo 5 a cikin injin motar bas mai lamba VDY 187 XA ranar Alhamis, 7 ga Maris 2024, a kan titin Gbongan-Ibadan da ke Jihar Osun bayan jami’anmu sun tsananta bincike.”

Babafemi ya ce “a yanzu haka an kama direban bas ɗin mai shekaru 35, inda aka bayar da ajiyarsa a gidan gyaran hali gabanin kammala bincike.”

A ranar Laraba, 6 ga watan Maris kuma, hukumar ta kama wata mata mai shekaru 26 da ake zargi da sayar da kayan maye.

Babban jami’in na NDLEA ya ce matar ta shiga hannu ne yayin wani samame da jami’ansu suka kai maboyarta a Osogbo, babban birnin Jihar Osun.

A Jihar Kano kuma, an kama wani matashi mai shekaru 35 da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 62 a Gadar Tamburawa, inda shi ma wani mai shekaru 40, ya shiga hannu da kwalaben maganin mura 244.

A ranar Alhamis, 7 ga watan Maris kuma, an kama wani mai shekaru 28, da ƙwayoyin tramadol guda 49,800 a kan titin Kano-Maiduguri.

A kwanakin baya ne Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Yobe, Mai Martaba Sarkin Fika, Dokta Muhammadu Abali Ibn Muhammadu Idrissa, ya bayyana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a matsayin abin da ke rura wutar rashin tsaro a jihohin Najeriya.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara