Connect with us

Labarai

Al’ummar Jigawa Sun Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Shirin Ciyarwa Na Watan Ramadan

Published

on

 

Al’ummomin Jihar Jigawa na ci gaba da nuna jin dadinsu dangane da bullo da ciniyoyin yin bude baki a watan Ramadan.

Wasu daga cikinsu da Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya zanta da su, da suka fito daga kananan hukumomin Dutse da Ringim da Hadejia da Gumel, da kuma Kazaure, sun bayyana cewar wannan hangen nesa da Gwamnan yayi zai matukar kawo masu sauki a wannan yanayi da ake ciki na hauhawar farashin kayan abinci.

Mallam Ali Bashir Kazaure da Dahiru Dutse sun nuna gamsuwa bisa cibiyoyin da gwamnatin jihar ta kafa domin ciyar da al’umma abincin bude baki.

Suma da suke tofa albarkacin bakin su, Malama Hansatu Sidi dake karamar hukumar Ringim da Talatu Abashe dake karamar hukumar Hadejia sun bayyana godiyarsu ga Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi bisa wannan tallafin kayayyakin abinci da aka fara kaddamarwa na rabawa al’ummar jihar.

Suna mai cewar shakka babu, suna samun tagomashi daga Gwamnati bisa tallafi da ake raba wa al’umma,  musamman  a kauyaku masu wahalar shiga.

Sai dai kuma, Malam Nura Usman Gumel yayi kira ga masu hannu da shuni da kungiyoyin da ba na gwamnati ba, da su taimakawa mutane da abinci a wannan watan na ramadan mai albarka.

Ya kuma bukaci al’umma da su rika tunawa gami da taimakawa marayu da abinci da suturu, domin samun lada a wajen Allah SWT.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kayayyakin da aka raba sun hada da buhunan shinkafa da masara dubu dari uku da katan din taliya dubu dari daya.

Kazalika, Gwamnatin jihar na sa ran mutane dubu dari daya da saba’in  da tara da da dari bakwai ne za su amfana  da tallafin ciyarwar a kowace rana na tsawon wata guda a jihar.

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara