Connect with us

Labarai

Ku Karanta Jerin Kamen Da Hukumar NDLEA Ta Yi A Farkon Watan Maris

Published

on

Jami’an Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa NDLEA reshen Jihar Borno, sun kama wasu dattawa biyu kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Hukumar ta bayyana cewa, daga cikin ababen zargin da suka shiga hannu akwai dattijo mai shekara 70 da kuma mai shekara 65.

Femi Babafemi, Daraktan yada labarai da bayar da shawarwari na NDLEA ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Ya ce, an kama wadanda ake zargin ne ranar Asabar 9 ga watan Maris tare da waɗanau matasa biyu — mai shekaru 24 da kuma mai shekaru 28 — a Maiduguri da Gamboru-Ngala.

A ranar Asabar ɗin kuma, jami’an NDLEA a Karamar Hukumar Geidam da ke Jihar Yobe, sun tare wata mota kirar Golf 3 da ke kan hanyar zuwa Gagamari a Jamhuriyar Nijar, inda aka kama wani matashi mai shekaru 28 zai kai tabar wiwi mai nauyin kilogiram 24.5 ga wani dila.

Hakazalika, hukumar ta ce a ranar Talata 5 ga watan Maris, ta kwace kwali 42 mai ɗauke da kwalabe 8,400 na maganin mura mai sa maye, da ke da nauyin kilogiram 1,260 a hannun wani direba mai shekaru 29 a hanyar Katsina.

Kakakin hukumar ya bayyana cewa, sun yi nasarar damke wani dilan haramtattun ƙwayoyin da ya ɓoye kayan mayen a injin wata motar bas.

Ya ce “Sun kama wani da wiwi da ta kai kilo 5 a cikin injin motar bas mai lamba VDY 187 XA ranar Alhamis, 7 ga Maris 2024, a kan titin Gbongan-Ibadan da ke Jihar Osun bayan jami’anmu sun tsananta bincike.”

Babafemi ya ce “a yanzu haka an kama direban bas ɗin mai shekaru 35, inda aka bayar da ajiyarsa a gidan gyaran hali gabanin kammala bincike.”

A ranar Laraba, 6 ga watan Maris kuma, hukumar ta kama wata mata mai shekaru 26 da ake zargi da sayar da kayan maye.

Babban jami’in na NDLEA ya ce matar ta shiga hannu ne yayin wani samame da jami’ansu suka kai maboyarta a Osogbo, babban birnin Jihar Osun.

A Jihar Kano kuma, an kama wani matashi mai shekaru 35 da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 62 a Gadar Tamburawa, inda shi ma wani mai shekaru 40, ya shiga hannu da kwalaben maganin mura 244.

A ranar Alhamis, 7 ga watan Maris kuma, an kama wani mai shekaru 28, da ƙwayoyin tramadol guda 49,800 a kan titin Kano-Maiduguri.

A kwanakin baya ne Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Yobe, Mai Martaba Sarkin Fika, Dokta Muhammadu Abali Ibn Muhammadu Idrissa, ya bayyana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a matsayin abin da ke rura wutar rashin tsaro a jihohin Najeriya.

Labarai

Labarai8 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara