Ilimi
Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
Gidauniyar Attahiru Bafarawa ta fara rabon tallafin kudi naira miliyan goma sha uku da dubu dari takwas ga iyaye mata marayu dari biyu da saba’in da bakwai da masu bukata ta musamman a jihar Sokoto domin tallafawa kananan sana’o’i.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin, Shugaban shirin, Malam Lawal Maidoki ya bayyana cewa, matakin ya yi daidai da kudurin wanda ya kafa na rage radadin tattalin arziki a tsakanin marasa galihu.
Ya bayyana cewa an zabo mutane 12 da suka ci gajiyar tallafin daga kowace karamar hukumar jihar 23 da suka hada da zawarawa 10 ko marayu mata da kuma nakasassu biyu a kowace karamar hukumar.
Ya ce kowane wanda ya ci gajiyar shirin zai karbi naira dubu hamsin tare da tallafin sufurin daga naira 3,000 zuwa naira 5,000, ya danganta da nisan su da wuraren rabon kayayyakin.
Maidoki ya jaddada cewa shirin na da nufin wadata wadanda suka samu tallafin jarin da ake bukata domin biyan bukatunsu na yau da kullum da kuma samar da kudaden shiga, da karfafa tattalin arzikin kasa.
Da yake jawabi a wajen taron, Sarkin Malaman Sokoto, Malam Yahaya Boyi, ya yabawa tsohon Gwamna, Alhaji Attahiru Bafarawa bisa wannan karamci da ya nuna.
Ya mika godiyar wadanda suka amfana, sannan ya bukace su da su yi addu’a ga masu hannu da shuni, Jihar Sakkwato, da Nijeriya, musamman a wannan wata na Ramadan mai albarka.
Boyi ya kuma ja hankalin wadanda suka karba da su yi amfani da kudaden da suka dace ta hanyar yin sana’o’i masu inganci maimakon yin bara.
Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin, Shehu Gwiwa, ya bayyana godiya a madadin sauran jama’a, inda ya gode wa wannan gidauniya bisa tallafin da ta bayar, ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa duk masu hannu a wannan shirin.
Nasir Malali
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
