Labarai
An Warware Rikicin Shugabancin Da Ya Dabaibaye Kungiyar Likitocin Zamfara
Kwamishinan lafiya na jihar Zamfara, Dr. Nafisa Muhammad Maradun, ta warware rikicin shugabancin kungiyar likitocin Najeriya NMA reshen jihar Zamfara.
Jami’in yada labarai, ma’aikatar lafiya. Sulaiman Isa ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce; Maradun tana magana ne a lokacin da ta karbi bakuncin kungiyar dattawan kungiyar reshen jihar Zamfara karkashin jagorancin Dr. Hassan Mamman a ziyarar ban girma da ya kai.
Kungiyar dattawan ta yaba da jajircewar Dr. Maradun da hangen nesa wajen jagorantar kungiyar likitocin Najeriya ta jaha a wannan lokaci mai cike da kalubale.
Taron ya kuma yi tsokaci kan tasirin sa hannun ta ga kungiyar da kuma tsarin kiwon lafiya baki daya a jihar.
Dakta Nafisa Maradun ta jaddada fifikon inganta fannin lafiya bisa tsarin ceton lafiyar al’umma na Gwamna Dauda Lawal.
Ta nuna jin dadinta da ziyarar kungiyar dattawan tare da jaddada kudurin yin aiki kafada da kafada da kungiyar likitocin domin cimma manufofin shirin ceto.
Ziyarar na nuna wani gagarumin mataki na karfafa hadin gwiwa tsakanin ma’aikatar lafiya da kwararrun likitoci a jihar.
REL/AMINU DALHATU/Wababe
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai7 days agoSojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
-
Labarai7 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai4 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai6 days agoNCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji
-
Labarai7 days agoNSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara
-
Labarai7 days ago’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa
-
Labarai4 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
