Labarai
Gwamnan Zamfara Ya Amince Da Bada Albashin Wata Daya Kyauta Ga Ma’aikatanta
Gwamna Dauda Lawal ya amince da biyan albashin wata daya kyauta da aka fi sani da 13th months ga ma’aikatan jihar Zamfara.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce shugaban ma’aikata na jihar ya sanar da amincewar ne a wata takardar da ya fitar a ranar 28 ga watan Disamban 2024.
Ta ce albashin shi ne irinsa na biyu a tarihin jihar Zamfara, inda gwamnatin Lawal Dauda ta biya na farko a watan Disambar bara.
Sanarwar ta ce, ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya za su samu alawus na kashi 30 bisa dari na albashinsu a matsayin albashinsu.
Sanarwar ta bayyana cewa, biyan alawus din na daya daga cikin dabaru da dama na karfafawa ma’aikata gwiwa da bunkasar tattalin arziki a jihar Zamfara.
Domin cika alkawuran da ta dauka, gwamnati ta biya sama da Naira biliyan 10 na giratuti da ake binta a cikin shekaru 11 da suka gabata, ta kuma amince da mafi karancin albashi na Naira 70,000, tare da tabbatar da biyan albashin ma’aikata kan lokaci.
Daga Aminu Dalhatu
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
