Connect with us

Labarai

’Yar Najeriya Ta Lashe Gasar Alkur’ani Ta Duniya

Published

on

’Yar Najeriya mai shekaru 19 mai suna Hajara Ibrahim Dan’azumi, ta lashe gasar karatun Alkur’ani ta Duniya ta bana.

Malama Hajara ta zama Gwarzuwar Shekara ce bayan da ta samu maki 99.5 a Gasar Hashimite ta Karatun Alkur’ani da Tajwidi ta Mata ta Duniya.

Hajara, wadda ta wakilci Najeriya, a gasar karatun Alkur’ani Izu 60 da Tajwidi, ta yi nasarar doke mahaddata Alkur’ani 40 daga kashe 38 da suka fafata a gasar.

Karo na 18 da aka gudanar da Gasar Karatun Alkur’ani ta Hashemite da gwamnatin kasar Jordan ta gudanar ta kuma karbi masaukin baki.

Malama Hajara dalibar aji biyu ce a Jami’ar Jihar Gombe da kuma Makarantar Islamiyya ta Abubakar Siddiq Islamiyya da ke jihar.

Kafin yanzu, Malama Hajara Dan’azumi ce ta zo ta hudu a rukunin haddar Izu 40 a gasar karatun Alkur’ani ta kasa karo na 34 da aka gudanar a Jihar Legas.

A waccan gasar ta samu maki 97.1 a yayin da kanwarta Maryam ta zo ta daya a rukunin Izu 10 da Tangimi; daya ‘yar uwarta Safiya kuma, ta zo ta 8 a rukunin Izu 40.

Mahaddata 41 daga kasashe 39 ne dai suka fafata a gasar da aka gudanar a kasar Jordan, wadda Hajara ta lashe.

Gwamnan jihar Gombe ya bayyana farin cikinsa tare da alfahari da wannan nasara da matashiyar ta samu a fannin Alkur’ani a duniya.

Ya bayyana jinjinarsa ga malamanta da kuma iyayenta bisa jajircewarsu da ta kai matashiyar ga wannan mataki na daukaka.

Mahaddata 41 daga kasashe 39 ne dai suka fafata a gasar da aka gudanar a kasar Jordan, wadda Hajara ta lashe.

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara