Labarai
Majalisar Kasa Ta Bukaci A Tsaurara Tsaro Wajen Hakar Ma’adinai
Majalisar dattijai ta yi kira da a kara tsaurara matakan tsaro da ka’idojin aiki kan ayyukan hakar ma’adinai a kasar.
Majalisar dattijai ta yanke wannan kuduri ne sakamakon wani kudiri da Sanata Muhammad Sani Musa Neja ta Gabas ya dauki nauyi tare da mayar da martani kan rugujewar wani wurin hakar zinari da aka yi a ranar Lahadi a Farin Doki a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja.
Wurin, wanda kamfanin African Mineral and Logistics Ltd ke gudanarwa, ya ruguje sama da masu hakar ma’adinai 50 a lokacin da aka yi ruwan sama yayin da ya binne kusan 30 daga cikinsu.
Sanata Sani Musa wanda ya gabatar da kudirin ya ja hankalin majalisa kan munin lamarin, inda ya kara da cewa yana kira da a gudanar da bincike a kan lamarin a wani yunkuri na “gano duk wasu kura-kurai da suka shafi ka’idojin tsaro da aiwatar da doka a fannin.”
Bashir Mayere/Abdurrahman/Khalifa/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
