Connect with us

Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

Published

on

Daga Bashir Meyere

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da bukatar Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, na neman rancen Naira Tiriliyan 1.15 domin cike gibin kasafin kudin shekarar 2025.

Amincewar ta biyo bayan gabatar da rahoton kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da lamuran bashi na cikin gida da na waje.

Yayin da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, wanda mataimakinsa Sanata Haruna Manu ya wakilta, ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2025 na Naira tiriliyan 59.99 da Majalisar ta amince da shi, ya karu da Naira tiriliyan 5.25 idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 54.74 da gwamnatin tarayya ta fara gabatarwa.

Ya ce an riga an amince da Naira tiriliyan 12.95 a cikin kasafin, wanda hakan ya bar gibin  Naira tiriliyan 1.147, abin da ya haifar da bukatar wannan shirin neman rance.

Kwamitin ya bai wa Majalisar shawarar  amincewa da rancen cikin gida na Naira tiriliyan 1.15 domin cike gibin da ya samo asali daga karin kudin kasafin.

Kwamitin ya kuma bukaci Ministar Kudi  da Ofishin Kula da Lamuran Bashi su tabbatar da cewa an aiwatar da rancen cikin tsari, tare da bin ka’idojin gaskiya,  da sharuɗɗan da suka dace.

Majalisar Dattawa ta kuma umurci kwamitinta mai kula da bashin cikin gida da na waje da ya rika sa ido kan yadda za a aiwatar da amfani da kudin da aka ciwo bashi.

Haka kuma, Ministar Kudi za ta rika mika rahoton kowane watanni uku kan halin da ake ciki, da amfani da kudaden, da yadda ake biyan basussuka, yayin da za a kai duk wani rahoton sabawa tsarin  ga Majalisar Dattawa domin daukar matakin doka da ya dace.

 

 

Labarai

Labarai2 hours ago

NHIA Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na...

Labarai7 days ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin...

Mafi Shahara