Connect with us

Labarai

Gwamnan Kano Ya Bada Ayukkan Kilomita 70 A Yankun Karkara 10

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da ababen more rayuwa da suka dace a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da aikin samar da tituna masu tsawon kilomita 70 a tsakanin al’ummomin karkara 10 a kananan hukumomin jihar guda uku, wanda ya gudana a Rijiyar Gwangwan da Mil Goma a karamar hukumar Dawakin Kudu, wanda ya kai kilomita kusan 15 aka za a gudanar a wurare biyu na Karamar hukumar.

 

Ya ce aikin, wanda aka gudanar da shi tare da hadin gwiwar Bankin Raya Musulunci (IsDB) da Asusun Rayuwa Na (LLF), na da nufin inganta hanyoyin shiga yankunan karkara da yankunan da ke kusa da birane.

 

Gwamnan ya ce aikin ya kai sama da Naira miliyan dubu 11, inda aka ware Naira Miliyan dubu 2.6 don titin Mil Goma zuwa Yankatsari mai tsawon kilomita 7.2 da kuma hanyoyin Rijiyar Gwangwan mai tsawon kilomita 7.5.

 

Ya bukaci al’ummomin da suka amfana da su yi amfani da hanyar yadda ya kamata, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu yana lalata kayayyakin bayan an kammala za a yi maganinsa da gaske.

 

Gwamna Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na aiwatar da ayyukan raya ababen more rayuwa masu canza rayuwa a yankunan karkara.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara