Labarai
An Gargadi Jama’a Su Guji Zama A Muhallin Da Babu Isashshen Iska
Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Asibitin Jihar Kano, Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya gargadi jama’a da su nisanci gidaje ko dakunan da ba su da isasun wuraren da iska zai shiga tare da kai rahoton duk wasu alamun da ba a saba gani ba a asibiti mafi kusa don daukar matakan da suka dace.
A cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta hukumar Samira Suleiman ta rabawa manema labarai ta ce, wani hadarin da mutane ke fuskanta ya hada da zazzabi mai tsanani, ciwon kai, amai da ciwon makogwaro, kasala da sauransu.
Ya ce ƙwararrun Ma’aikatan Lafiya (RRT) suna zaman ko ta kwana duk wuraren kiwon lafiya don magance duk wani al’amarin da ya taso na gaggawa.
“Saboda sauye-sauyen yanayi da cututtuka masu yawa, babban sakataren hukumar kula da asibitocin jihar Kano Dakta Mansur Mudi Nagoda yana shawartar jama’a da su yi taka tsantsan tare da ziyartar asibiti mafi kusa da zarar sun kamu da wata alama da ba a saba gani ba don guje wa bugun jini da ciwon sankarau.
“Wasu daga cikin alamomin sun haɗa da, Zazzaɓi mai tsanani, ciwon kai, amai da ciwon makogwaro, gajiya da lallashi kamar sauran alamomin.
Abdullahi Jalaluddeen Kano/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
