Kasuwanci
Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano
Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma wajen dakile yaduwar kwarin nan da ke lalata tumatur a gonaki.
Shugaban ya yi wannan kiran ne a wata hira da gidan rediyon Najeriya a Kano.
A cewar sa, kwarin sun mamaye gonakin tumatir a kananan hukumomin Bagwai da Shanono da Kura da Garin Malam da Bebeji, Bunkure da Rano da Kibiya da kuma wasu sassan Tudun Wada Dawakin Kudu.
Maibreadi ya bayyana cewa, rahoton da AFAN ta samu daga sassan kananan hukumomin ya nuna cewa gonakin Tumatir da suka kai hekta dubu hudu da dari shidda da ashirin da daya da kudinsu ya kai Naira biliyan daya ne a halin yanzu suka kamu da cutar, yana mai jaddada cewa idan ba a yi wani abu don ceto lamarin ba, nan da mako daya zuwa biyu masu zuwa, manoma za su yi asarar kusan Naira miliyan dubu goma zuwa dubu ashirin a Kano.
“Abin takaici shine akasarin manoman sun gama kashe kudi a gonakinsu, kuma shuka ta yi kyau, an kusa girbi sai kuma ga cutar ta bulla.”
Maibreadi ya jaddada bukatar gwamnati ta taimaka wa manoma da ingantaccen iri mai jure wa yanayi, yana mai cewa, manoman Kubewa suma sun sami bullar irin wannan annoba a kakar noman da ta gabata.
“Mu manoma ba mu da ikon samun wadannan irin shuka, amma idan gwamnati ta hada hannu da kamfanonin kasa da kasa, za su iya saye su sayar da su, ko kuma ba da tallafi ga manoma domin gujewa irin wannan babbar asara da ke kara shafar tattalin arzikin kasar.”
Shugaban ya bukaci manoma da su daina amfani da maganin kwari mara inganci domin gujewa asara.
Khadija Aliyu
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar