Kasuwanci
Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano
Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma wajen dakile yaduwar kwarin nan da ke lalata tumatur a gonaki.
Shugaban ya yi wannan kiran ne a wata hira da gidan rediyon Najeriya a Kano.
A cewar sa, kwarin sun mamaye gonakin tumatir a kananan hukumomin Bagwai da Shanono da Kura da Garin Malam da Bebeji, Bunkure da Rano da Kibiya da kuma wasu sassan Tudun Wada Dawakin Kudu.
Maibreadi ya bayyana cewa, rahoton da AFAN ta samu daga sassan kananan hukumomin ya nuna cewa gonakin Tumatir da suka kai hekta dubu hudu da dari shidda da ashirin da daya da kudinsu ya kai Naira biliyan daya ne a halin yanzu suka kamu da cutar, yana mai jaddada cewa idan ba a yi wani abu don ceto lamarin ba, nan da mako daya zuwa biyu masu zuwa, manoma za su yi asarar kusan Naira miliyan dubu goma zuwa dubu ashirin a Kano.
“Abin takaici shine akasarin manoman sun gama kashe kudi a gonakinsu, kuma shuka ta yi kyau, an kusa girbi sai kuma ga cutar ta bulla.”
Maibreadi ya jaddada bukatar gwamnati ta taimaka wa manoma da ingantaccen iri mai jure wa yanayi, yana mai cewa, manoman Kubewa suma sun sami bullar irin wannan annoba a kakar noman da ta gabata.
“Mu manoma ba mu da ikon samun wadannan irin shuka, amma idan gwamnati ta hada hannu da kamfanonin kasa da kasa, za su iya saye su sayar da su, ko kuma ba da tallafi ga manoma domin gujewa irin wannan babbar asara da ke kara shafar tattalin arzikin kasar.”
Shugaban ya bukaci manoma da su daina amfani da maganin kwari mara inganci domin gujewa asara.
Khadija Aliyu
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
