Connect with us

Kasuwanci

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Published

on

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma wajen dakile yaduwar kwarin nan da ke lalata tumatur a gonaki.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a wata hira da gidan rediyon Najeriya a Kano.

A cewar sa, kwarin sun mamaye gonakin tumatir a kananan hukumomin Bagwai da  Shanono da  Kura da  Garin Malam da Bebeji, Bunkure da Rano da  Kibiya da kuma wasu sassan Tudun Wada Dawakin Kudu.

Maibreadi ya bayyana cewa, rahoton da AFAN ta samu daga sassan kananan hukumomin ya nuna cewa gonakin Tumatir da suka kai hekta dubu hudu da dari shidda da ashirin da daya da kudinsu ya kai Naira biliyan daya ne a halin yanzu suka kamu da cutar, yana mai jaddada cewa idan ba a yi wani abu don ceto lamarin ba, nan da mako daya zuwa biyu masu zuwa, manoma za su yi asarar kusan Naira miliyan dubu goma  zuwa dubu ashirin a Kano.

Abin takaici shine akasarin manoman sun gama kashe kudi a gonakinsu, kuma shuka ta yi kyau, an kusa girbi sai kuma ga cutar ta bulla.”

Maibreadi ya jaddada bukatar gwamnati ta taimaka wa manoma da ingantaccen iri mai jure wa yanayi, yana mai cewa, manoman Kubewa suma sun sami bullar irin wannan annoba a kakar noman da ta gabata.

Mu manoma ba mu da ikon samun wadannan irin shuka, amma idan gwamnati ta hada hannu da kamfanonin kasa da kasa, za su iya saye su sayar da su, ko kuma ba da tallafi ga manoma domin gujewa irin wannan babbar asara da ke kara shafar tattalin arzikin kasar.”

Shugaban ya bukaci manoma da su daina amfani da maganin kwari mara inganci domin gujewa asara.

Khadija Aliyu

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara