Labarai
Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Kano Ta Sake Gurfanar Da Ganduje Gaban Kuliya
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauraron korafe-korafen jama’a ta jihar Kano ta shigar da sabbin tuhume-tuhume kan almundahana a kan tsohon gwamnan jihar Dr. Abdullahi Ganduje.
Shugaban Hukumar, Muhuyi Magaji ne ya bayyana hakan a shirin da yayi a wani gidan talabijin mai zaman kasa a ranar Talata, inda ya zargi gwamnatin Ganduje da karkatar da kudaden al’umma.
Ya bayyana cewa, bincike ya nuna yadda aka karkatar da naira biliyan hamsin da dayada miliyan dari uku na kudaden kananan hukumomi zuwa wasu asusun ajiya da basu da hurumin karbar irin wadannan kudaden.
A cewar Muhuyi, gwamnatin Ganduje na cire naira biliyan 1 a duk wata daga asusun jihar ba bisa ka’ida ba.
Ya kuma yi ikirarin cewa, an zuba Naira biliyan 4 ga asusun wani kamfanin noma daga asusun tattara harajin jihar ba tare da wani dalili ba.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato