Connect with us

Fasaha

Za Mu Hukunta Duk Wanda Aka Samu Yana Cin Zarafin Almajirai – Hukumar Almajirai Ta Kasa

Published

on

 

Sakataren zartarwa na Hukumar Almajirai ta kasa Dr Muhammad Sani Idris ya ce gwamnatin tarayya ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu yana cin zarafin Almajirai a kowane bangare na kasar nan.

 

Dr Mohammad Sani Idris ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ziyarci wani yaro Almajiri da ake zargin an zalunce shi kuma yana jinya a Asibitin kasi da ke Dala Kano.

 

Ya ce gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin ba a ci zarafin yara da ba su zuwa makaranta da kuma Almajirai ba.

 

Dokta Mohammed Sani Idris ya ce makasudin ziyarar tasa shi ne don jajanta wa yaron da iyalansa, da kuma sanar da jama’a cewa za a hukunta wanda ya aikata wannan danyen aikin don tabbatar da adalci.

 

Sakataren zartaswar ya bayyana cewa hukumar za ta bi diddigin lamarin domin ganin an hukunta wanda ya aikata hakan kamar yadda doka ta tanada.

 

 

Dakta Mohammad Sani Idris ya ci gaba da cewa hukumar ta himmatu wajen inganta Almajirai da kuma ba da ilmin makarantu da nufin ganin yadda harkar barace-barace da kuma rashin zuwa makaranta Yara sun zama tarihi.

 

 

Ya kuma ba da tabbacin gwamnati mai ci ta himmatu wajen magance kalubalen da ‘ya’yan Almajirai ke fuskanta a kasar nan.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara