Kasuwanci
Za A Sabunta Filin Jiragen Sama Na Ilori Zuwa Cibiyar Jigilar Kayayyaki Ta Zamani
Gwamnatin Jihar Kwara ta ce za ta yi haɗin gwiwa da Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN) da sauran masu ruwa da tsaki domin mayar da jihar cibiyar fitar da kayan gona da na kasuwanci.
Kwamishinan Noma da Ci gaban Karkara na jihar, Dakta Afees Abolore, ne ya bayyana haka a wani taron da Hukumar FAAN ta shirya domin sanar da shirin fara jigilar kayayyaki a Filin Jiragen Sama na Ƙasa da Ƙasa na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilori.
A cewarsa, wannan shiri na nufin kara inganta matsayin jihar tare da ƙarfafa rawar da take takawa a harkokin kasuwanci na cikin gida da waje.
Ya jaddada cewa aikin ya yi daidai da manufofin wannan gwamnati na buɗe sababbin hanyoyin fitar da kayayyaki, bunƙasa harkokin kasuwanci, da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga ga masu samar da kayayyaki da ‘yan kasuwa.
Dakta Abolore ya ce jigilar kayayyakin ta jiragen zai sauƙaƙa daukarsu daga gonaki, zuwa masana’antu, da wuraren sana’o’i zuwa kasuwannin cikin gida da na ƙasashen waje, wanda hakan zai ƙara musu daraja, sarrafawa da a fannoni daban-daban.
Kwamishinan ya bayyana cewa shirin zai rage asara, ya kiyaye ingancin kayayyaki, sannan ya bunƙasa damar kasuwanci a fannin kayayyakin gona, masana’antu, da kayayyakin da aka sarrafa.
Ya nuna cewa saboda cunkoson da ake samu a tashoshin jiragen sama da na ruwa da ke Legas, garin Ilori na wata dama ta musamman wajen samun fitar da kayayyaki cikin lokaci da inganci, tare da ƙara wa jihar damar gogayya da jihohi da ma kasashen duniya.
Dakta Abolore ya yi kira ga manoma, ƙungiyoyi, masu masana’antu, masu saka jari, ƙungiyoyin sufuri, ‘yan kasuwa, masu sarrafawa, da hukumomin da ke kula da doka da tsari, da su haɗa kai wajen kara inganci, yadda ake shirya kayayyaki daidai da zamani, da amfani da fasaha domin bin ka’idojin kasuwannin ƙasashen waje.
Shi ma Manajan Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idiagbon, Mista Suraju Aderibigbe, ya bayyana cewa za a sabunta tsohon ginin tashar zuwa sabuwar cibiyar jigilar kaya mai amfani da fasahohi na zamani domin tabbatar da tsaro wajen sarrafa nau’ukan kayayyaki daban-daban.
Ya tabbatar da cewa wannan gyara zai ƙara bunƙasa kasuwanci, samar da ayyukan yi, da kuma ci gaban tattalin arziki a fannoni da dama a jihar.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
