Connect with us

Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbe Wani Basarake A Jihar Taraba

Published

on

A safiyar Juma’a 19 ga watan Afrilun 2024, al’ummar masarautar Sansani da ke karamar hukumar Gassol a jihar Taraba suka wayi gari da mummunan labarin kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa Basarake Abdulmutallib Nuhu.

Wannan lamari ya faru ne ‘yan sa’o’i kadan kafin a fara bikin kamun kifi na Nwonyo, wanda ya shafe shekaru 14 ba a yi ba, sai a wannan lokaci da gwamnatin Gwamna Agbu Kefas ta sake farfado da shi.

An shirya gudanar da bikin ne a karamar hukumar Ibi ta jihar, kusa da kogin Benue a kudancin jihar ta Taraba.

Sansani yana da nisan kilomita kaɗan daga karamar hukumar Ibi, wurin da aka keɓe don bikin Kamun Kifin na Nwonyo.

A cewar Danmasanin Sansani, Salihu Sansani, kuma  yayan marigayin, ‘yan bindigar sun isa garin Sansani ne da misalin karfe 9 na daren ranar Alhamis, inda suka doshi fadar kai tsaye suka kashe sarkin.

Ya shaida wa manema labarai cewa maharan sun zo ne a kan babura, inda suka harbe dan uwansa, sannan suka arce da wayoyinsa guda biyu.

A yayin da suke barin kauyen, sun ci karo da wani matashi a kan babur, inda  suka harbe shi a kafa.” in ji Danmasani.

Sai dai wani babban jami’in ‘yan sanda da ke aiki a yankin Sansani ya shaida wa wakilinmu cewa tuni rundunarsa ta fara bibiyar wadanda suka kashe babban basarake.

A lokacin hada wannan rahoto, Mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, ASP James Lashen, ya bayyanawa manema labarai ta wayar tarho cewa yana kan hanyarsa ta zuwa ofishin don sanin halin da ake ciki game da lamarin.

Sani Sulaiman

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara