Labarai
Gwamna Kefas Na Taraba Ya Karbi Katin Jam’iyyar APC
Daga Jamila Abba
Gwamnan Jihar Taraba, Dakta Agbu Kefas, ya karɓi katin shaidar zama dan jam’iyyar APC a hukumance, wanda hakan ya tabbatar da cikakken rajistarsa cikin jam’iyyar.
An mika katin membobinsa na APC ga Gwamnan ne ta hannun Shugaban APC a gundumar Asibiti (Hospital Ward) da ke Karamar Hukumar Wukari, Honarabul Umaru Tanko ne ya mika katin zama mamban na APC ga Gwamna Kefas a gidan TY Danjuma da ke Jalingo.
Da yake jawabi a ofishinsa bayan karɓar katin, Gwamna Kefas ya bayyana cewa rajistarsa ta tabbatar da matsayinsa a hukumance a matsayin cikakken mamba na APC, wanda hakan zai ba shi damar shiga dukkan harkokin jam’iyyar.
Ya ƙara da cewa nan ba da jimawa ba za a yi bikin sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar ta APC.
A yayin mika katin, Honarabul Umaru Tanko ya bayyana Gwamnan a matsayin cikakken mamba na APC tare da nuna farin cikin jam’iyyar na maraba da shi a hukumance.
Haka kuma, Kwamishinar yada Labarai da Wayar da Kai ta Jihar, Barista Zainab Usman Jalingo, ta tabbatar da cewa yanzu Gwamna Kefas cikakken mamba ne na APC a Jihar Taraba.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
