Labarai
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba Wa Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
Daga Aminu Dalhatu
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Shugaban Karamar Hukumar Gusau, Alhaji Abubakar Imam, bisa shirin tallafawa jama’a domin dogaro da kai da kuma inganta rayuwarsu.
Ta yi wannan yabo ne yayin bikin kaddamar da kayan tallafi a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta bayyana cewa, kayayyakin da aka raba sun haɗa da motoci, babura, injinan dinki, injinan niƙa, keken guragu, kayan abinci da kuma tallafin kuɗi a fadin ƙaramar hukumar.
Ta bayyana shirin a matsayin abin yabo da ke tallafawa iyalai, wanda ke karfafa dogaro da kai, tare da rage matsin tattalin arziki a tsakanin al’umma.


Uwargidan Gwamnan ta taya waɗanda suka amfana da shirin murna, tare da shawartarsu da su yi amfani da kayan yadda ya kamata domin inganta rayuwarsu da kuma bayar da gudunmawa wajen ci gaban al’umma.
A wani bangare kuma, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta karɓi tawagar mata da suka sauya sheƙa daga jam’iyyun siyasa daban-daban zuwa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai mulki.

Uwargidan Gwamnan ta tabbatar wa sabbin mambobin jam’iyyar da cewa za a ba su dama da haɗin kai a dukkan harkokin jam’iyya, tare da kira gare su da su ba da goyon baya ga hangen nesan gwamnatin wajen tabbatar da zaman lafiya, ci gaban tattalin arziki da dorewar cigaba a fadin jihar.
A nata jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Gusau, Alhaji Abubakar Imam, ya ce an shirya wannan tallafin ne domin taimakawa masu buƙata su dogaro da kansu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
