Ilimi
Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don gudanar da aikin hajjin bana na 2024 zuwa Saudiyya a ranar Talata 21 ga watan Mayu.
Sanarwar da Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kwara, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ya fitar, ta ce an samu canjin ranar ne sakamakon tsaikon da aka samu daga bangaren NAHCON da kamfanonin jiragen sama.
A cewar sanarwar Alhazan jihar Kwara da farko an shirya yin jigilarsu na farko a ranar Litinin 20 ga Mayu, 2024.
Sanarwar ta shawarci maniyyatan su zo sansanin alhazai litinin din kafin fara jigilar su a ranar Talata da karfe 10:20 na safe.
A halin da ake ciki Mai Martaba Sarkin Ilorin Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari ya bukaci maniyyatan da su yi amfani da lokacin gudanar da aikin Hajjin bana wajen gudanar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, hadin kai da ci gaban tattalin arzikin kasa.
Alhaji Sulu-Gambari ya bayyana haka ne a sakon sa na fatan alheri ta hannun mai magana da yawunsa, Mallam Abdulazeez Arowona.
Ya kuma umarce su da su yi amfani da damar ziyarar da zasu kai garuruwan Madina da Makkah na kasar Saudiyya a wannan lokaci mai albarka a matsayin babban abin alfahari na neman kusanci ga Allah Madaukakin Sarki.
Mai martaba Sarkin ya roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ba dukkan alhazai lafiya da basira domin gudanar da ayyukan Hajji cikin nasara.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU/Wababe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
