Connect with us

Ilimi

Sudan ta Kudu ta Rufe Makarantun Kasar Saboda Tsananin Zafi

Published

on

Gwamnatin Kasar Sudan ta Kudu ta sanar da cewa za ta rufe duka makarantun ƙasar daga ranar Litinin sakamakon tsananin zafin da ake fargabar ƙasar za ta fusakanta.

Ma’aikatun ilimi da na lafiya sun bayar da shawara ga iyayen yara kan yara su zauna a gida sakamakon ana fargabar zafi a ƙasar zai kai har maki 45 a ma’aunin Celsius.

Ma’aikatun sun yi gargaɗi kan cewa duk wata makaranta da aka kama a buɗe za ta fuskanci hukunci wanda hakan zai iya kaiwa ga har a ƙwace lasisinta.

Duk da cewa ma’aikatun ba su sanar da tsawon lokacin da makarantun za su kasance a rufe ba, amma hasashen yanayi ya nuna cewa za a shafe kusan mako biyu ana fuskantar wannan zafin.

Ma’aikatun sun ce za su ci gaba da sanya ido kan lamarin tare da sanar da jama’a yadda ya kamata.

Peter Garang, wani mazaunin Juba babban birnin kasar, ya yi maraba da matakin.

Ya ce “ya kamata a saka wutar lantarki a makarantu” domin a samu damar shigar da na’urorin sanyaya ɗaki.

Sudan ta Kudu wadda tana daga cikin sabbin ƙasashe a duniya, na fama da matsalar sauyin yanayi tare da tsananin zafi na gama gari amma ba kasafai yake kai maki 40 ba a ma’aunin Celcius.

Rikicin cikin gida dai ya addabi kasar da ke gabashin Afirka wadda ita ma take fama da fari da ambaliyar ruwa, lamarin da ya jefa mazauna kasar cikin wahala.

AP

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara