Connect with us

Labarai

Sudan ta Kudu ta Bai wa Fararen Hula Umarnin Barin Yankunan da ke Hannun ‘Yan Adawa

Published

on

Rundunar Sojin Sudan ta Kudu ta bai wa fararen hula da ƙungiyoyin agaji da ma’aikatan Majalisar Ɗinkin Duniya wa’adin sa’o’i 48 su bar yankunan da ke ƙarƙashin ikon ‘ƴan adawa a jihar Jonglei da ke gabashin ƙasar, gabanin fara wani babban farmakin soji.

Wannan umarni na zuwa ne kwanaki biyu bayan da babban hafsan sojin ƙasar ya shaida wa dakarunsa cewa suna da kwanaki bakwai su “murƙushe tawaye” a gabashin ƙasar, wanda hukumomi suka ce na iya zama barazana ga babban birnin ƙasar, Juba.

A cikin wani faifan bidiyo da ya fitar a ranar Lahadi, kakakin rundunar sojin Sudan ta Kudu SSPDF, Manjo Janar Lul Ruai Koang ya ce dole ne mutanen da ke zaune a yankunan da ke hannun ƙungiyar ƴan adawa ta Sudan wato SPLA-IO, su fice cikin wa’adin da aka bayar.

Ya ƙara da cewa dole ne kuma fararen hula su koma yankunan da ke ƙarƙashin ikon gwamnati domin tsaron lafiyarsu, yayin da sojoji ke shirin ƙaddamar da farmakin da suka sanya wa suna da “Dorewar Zaman Lafiya”.

Kakakin ya kuma yi gargaɗin cewa duk fararen hula masu ɗauke da makamai su miƙa su ga sojojin gwamnati, yana mai cewa duk wanda aka samu kusa da barikin ƴan adawa SPLA-IO za a ɗauke shi a ɗaya daga cikinsu a haɗa da shi a farmakin.

Ƙungiyar ƴan adawa SPLA-IO ba ta ce komai ba dangane da wannan Umurnin.

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara