Labarai
Shugaba Tinubu ya Ayyana Masu Garkuwa da Mutane a Matsayin Yan ta’adda
Shugaban Kasar Nijeriya Ahmed Bola Tinubu ya bayyana cewa ya zama dole a riƙa ɗaukan mutanen da ke da hannu a aikata miyagun laifuka a matsayin ƴan ta’adda.
Shugaban ya bayyana haka ne ranar Talata a taron buɗe-baki tare da ma’aikatan shari’a na gwamnatin tarayya bisa jagorancin alƙalin alƙalai na ƙasa, mai shari’a Olukayode Ariwoola.

Da yake nanata ƙudirin gwamnati na murƙushe ƴan bindiga, shugaba Tinubu ya ce waɗanda suke sace yara matsorata ne da ba za su iya gaba da gaba da sojojin Najeriya ba.
“Dole ne mu ayyana masu garkuwa a matsayin ƴan ta’adda,” in ji shugaban ƙasar, kamar yadda wata sanarwa da kakakinsa Ajuri Ngelale ta ruwaito.
Bello WAKILI
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
