Connect with us

Fasaha

Shirin Fitar ‘Yan Nijeriya Miliyan 50 Daga Talauci Zai Tabbata – Idea Lab

Published

on

Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar kungiyar Idea Lab sun tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa shirin da gwamnatin yanzu ta yi na fitar da ‘yan Nijeriya miliyan hamsin daga kangin fatara zai kasance gaskiya.

 

Kungiyar Idea Lab Agency tare da hadin gwiwar Bankin Masana’antu, Babban Bankin Najeriya da sauran Hukumomin Gwamnati sun kuduri aniyar ganin an cimma wannan kyakkyawar manufa ta Shugaba Bola Ahmad Tinubu kafin 2027.

 

Babban jami’in kungiyar Idea Lab Organisation Mr Rex Emmanual ya bayyana haka a lokacin da yake yiwa manema labarai karin haske kan ayyukan kungiyar kan shirye-shiryen raya kasa.

 

Mista Rex ya ce Idea.Lab tare da hadin gwiwar Bankin Masana’antu, Babban Bankin Najeriya da Bankin Duniya suna zaburar da ‘yan kasa don sanin yadda ake samun tallafi da lamuni a fadin duniya don bunkasa tattalin arziki ta hanyar kanana da matsakaitan masana’antu.

 

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tana haɗin gwiwa tare da wasu cibiyoyi na kuɗi a matsayin ingantattun dandamali don bada duk tallafi kuma a shirye suke su ga ‘yan Najeriya masu sha’awar Tattalin Arziki na Kasuwancin zamani ya tabbata.

 

Mista Rex ya ci gaba da bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kirkiro wannan tsarin ne domin amfanin kananan kamfanoni da matsakaitan masana’antu don samun irin wannan lamuni.

 

Babban kodinetan na kasa ya yi imanin cewa hakan zai taimaka wajen fitar da ‘yan Najeriya miliyan hamsin daga kangin talauci bisa manufar gwamnatin tarayya.

 

A cewar kodinetan na kasa, shirin na Lab yana da goyon bayan Bankin Masana’antu da Gwamnatin Tarayyar Najeriya don horar wa, shiryawa da daukar wakilai da masu cin gajiyar ayyukan yi a cikin gida da waje.

 

Ya ce babban bankin kasar da sauran bankunan kasuwanci sun shigo ne saboda shirin ya kunshi kudi, don haka mutane za su iya samun lamuni ta hanyar wakilai da taimakon tallafin karatu da sauran ayyukan fasaha.

 

Bashir Mayere/Wababe

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara