Connect with us

Labarai

Sarkin Birnin Gwari Ya Yaba da Tsarin Zaman Lafiya A Yankinsa, Yayi Kira Ga Manoma Su Ci Gaba Da Noma

Published

on

Sarkin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Jibril Maigwari ya yaba da nasarar tsarin zaman lafiya da aka kaddamar a yankin kusan watanni goma da suka gabata, yana mai cewa ya dawo da kwanciyar hankali tare da karfafa wa manoma gwiwa su koma gonakinsu.

 

Da yake magana a lokacin ziyarar gani da ido domin duba yadda tsarin zaman lafiya yake a Birnin Gwari, Sarkin ya ce yarjejeniyar zaman lafiya—wadda ta samu da haɗin gwiwar Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA), Gwamnatin Jihar Kaduna, hukumomin tsaro da kuma wakilan ƙungiyoyin ’yan bindiga—ya taimaka sosai wajen rage matsalar rashin tsaro a yankin.

 

Ya bayyana cewa ko da yake har yanzu ana samun yan kwace kwace daga wasu miyagu amma lamarin tsaron yayi sauƙi sosai idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

Sarkin ya bayyana cewa a tarukan da aka gudanar da shugabannin al’umma, an shawarci manoma su koma gonakinsu duk da kalubale, ko da hakan na nufin amfani da taki na gargajiya a maimakon na zamani.

 

A cewarsa, da dama daga cikin manoma sun bi wannan shawara, abin da ya haifar da dawowar ayyukan noma a yankin saboda zaman lafiya da aka samu.

 

Alhaji Zubairu Maigwari ya jaddada cewa nan da shekara mai zuwa, ana sa ran karin manoma za su koma cikakke gonakinsu idan zaman lafiya ya ci gaba da inganta.

 

A tattaunawa da aka yi da Danmasanin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu AbdurRauf, ya bayyana cewa tsarin zaman lafiyar ya samar da damar zama tare, inda makiyaya da manoma ke aiki tare domin kare wannan yarjejeniya.

 

Ya kara da cewa harkokin tattalin arziki sun fara farfaɗowa a Birnin Gwari, inda al’ummomi da kansu ke taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya.

 

Ya kuma roki Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna su faɗaɗa tsarin zuwa wasu wurare masu fama da rikice-rikice, musamman ƙauyukan kan iyaka da ke fuskantar barazanar shiga daga jihohin makwabta.

 

Ya jaddada cewa irin tsarin tabbatar da zaman lafiya da akayi a Birnin Gwari zai taimaka wajen dakile matsalolin tsaro a yankunan kan iyaka tare da ƙarfafa ƙoƙarin zaman lafiya a fadin ƙasar nan.

 

A halin yanzu, an ziyararce yammacin Birnin Gwari—ciki har da Dam ɗin Fagoma da Sabon Layi da Gagumi da Kakangi da Kuma Randagi domin duba yadda manoma suka koma gonakinsu.

 

A matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar, tsoffin ’yan bindiga da al’ummomin yankin ana sa ran za su tashi tsaye domin kare yankinsu daga dukkan wani kallubalen tsaro.

PR: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara