Labarai
Rundunar ‘Yan Sanda ta Kebbi Ta Kama Dan Damfara
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Hamza Abdullahi Sama, mazaunin unguwar KCC a Birnin Kebbi, bisa zargin damfarar sama da mutum 175 da ke neman aikin yi, a ƙarƙashin hujjar samar musu da ayyukan shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da gwamnatin jiha ta amince da su.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
SP Bashir ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya yi karya ta hanyar bayyana kansa a matsayin wanda Gwamnatin Jihar Kebbi ta bashi damar shirya daukar ma’aikata a makarantun firamare da sakandare.
Ya ce bisa wannan ƙaryar wakilci, waɗanda abin ya shafa—ciki har da Shafa’atu, Yusuf Yahaya, Hussaini Sani, Ubaida Abubakar, da sauransu sun yarda suka biya Naira dubu talatin kowanne, a matsayin kudaden kafin alkalami na wasu abubuwa kafin basu aikin.
SP Bashir ya ƙara da cewa ƙarin bincike ya tabbatar da cewa wanda ake zargin ya damfari jimillar Naira miliyan 5 da dubu 200 daga hannun waɗanda abin ya shafa, ta hanyar yaudara da gangan, domin babu irin waɗannan guraben aiki, kuma ba a ba shi izini daga kowace hukuma ta gwamnati ba don ɗaukar ma’aikata ko sarrafa ayyuka a madadinta.
A halin yanzu, wanda ake zargin na tsare a hannun ‘yan sanda, kuma bincike na ci gaba da gudana da nufin gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike. Rundunar ta kuma ja hankalin al’umma da su kasance masu faɗake da taka-tsantsan daga mutanen da ke cin moriyar halin ƙunci na masu neman aiki ta hanyar shirya aikin yi na bogi.
SANI DUTSINMA
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
