Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yan Sanda ta Kebbi Ta Kama Dan Damfara

Published

on

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Hamza Abdullahi Sama, mazaunin unguwar KCC a Birnin Kebbi, bisa zargin damfarar sama da mutum 175 da ke neman aikin yi, a ƙarƙashin hujjar samar musu da ayyukan shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da gwamnatin jiha ta amince da su.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

SP Bashir ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya yi karya ta hanyar bayyana kansa a matsayin wanda Gwamnatin Jihar Kebbi ta bashi damar shirya daukar ma’aikata a makarantun firamare da sakandare.

Ya ce bisa wannan ƙaryar wakilci, waɗanda abin ya shafa—ciki har da Shafa’atu, Yusuf Yahaya, Hussaini Sani, Ubaida Abubakar, da sauransu sun yarda suka biya Naira dubu talatin kowanne, a matsayin kudaden kafin alkalami na wasu abubuwa kafin basu aikin.

SP Bashir ya ƙara da cewa ƙarin bincike ya tabbatar da cewa wanda ake zargin ya damfari jimillar Naira miliyan 5 da dubu 200 daga hannun waɗanda abin ya shafa, ta hanyar yaudara da gangan, domin babu irin waɗannan guraben aiki, kuma ba a ba shi izini daga kowace hukuma ta gwamnati ba don ɗaukar ma’aikata ko sarrafa ayyuka a madadinta.

A halin yanzu, wanda ake zargin na tsare a hannun ‘yan sanda, kuma bincike na ci gaba da gudana da nufin gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike. Rundunar ta kuma ja hankalin al’umma da su kasance masu faɗake da taka-tsantsan daga mutanen da ke cin moriyar halin ƙunci na masu neman aiki ta hanyar shirya aikin yi na bogi.

SANI DUTSINMA

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara