Labarai
Rukunin Farko Na Alhazan Jihar Borno Ya Isa Madina
Rukunin farko na maniyyata 383 daga jihar Borno ya isa garin kasa mai tsarki da safiyar yau Litinin tare da ragowar maniyyata 27 daga jihar Yobe.
Jihar Borno na da jimillar maniyyata 1,815 da ake sa ran za a yi jigilar su zuwa aikin Hajjin bana.
Da yake jawabi ga rukunin na farko na maniyyatan a filin jiragin sama na Muhammadu Buhari da ke Maiduguri, mataimakin gwamnan jihar Borno, Alhaji Umar Kadafur ya bukace su da su bi dokokin kasar Saudiyya sau da kafa.
Ya kuma bukace su da su yi addu’ar samun dauwamamman zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.
A wata hira da gidan rediyon Najeriya a Maiduguri, mukaddashin shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno, Alhaji Dawule Mainok ya ce rukunin na farko ya kunshi maza 234 da mata 149.
Ya yi kira ga maniyyatan da su kasance jakadu nagari yayin da suke kasa mai tsarki.
Biyu daga cikin mahajjatan Aisha Ali daga Ngala da Idris Allamin daga karamar hukumar Konduga sun bayyana aikin tantancewar a matsayin maras cikas, sun yabawa hukumar alhazai ta kasa da hukumar alhazai ta jiha bisa jajircewa wajen ganin komi ya tafi yadda ake bukata.
Dauda Iliya
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
