Labarai
RSF da rundunar sojin Sudan sun kashe mutum 190 a Darfur
Ƙungiyar likitocin Sudan ta zargi sojojin ƙasar da dakarun RSF da kashe kusan mutum 200 a gumurzun da suke yi a wasu yankuna da ke yankin Dafur, kamar yadda jaridar intanet ta Sudan Tribute ta ruwaito.
“Rahoton ƙungiyar ya gano an kashe mutum 190, sannan an jikkata wasu guda 106 a sanadiyar ruwan bama-bamai a tsakanin ɓangarorin biyu a kudanci da arewacin Dafur a ƴan kwanakin nan.”
Rahoton ya nuna cewa dakarun RSF sun kashe sama da mutum 30, ciki har da mata da ƙananan yara a al-Fashir, sannan sojoji sun kashe mutum 115 a Kabkabiya da wasu mutum 45 a Nyala a kudancin Dafur.
A ƴan makonnin da ake ciki, sojojin Sudan sun ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare a kan dakarun RSF a Dafur.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
