Connect with us

Labarai

Rashin Wakilci Nagari: Al’ummar Kauru Sun Ce A’a ga Wa’adi na 3 na Muktar Chawai

Published

on

Siyasa na da wata hanya ta bayyana ainihin niyya ta hanyar lokaci. Taron da ɓangaren Hon. Mukhtar Zakari Chawai ya shirya kwanan nan, wanda aka sanya wa suna “APC Strategic Engagement Kauru Local Government”, ya zo ne jim kaɗan bayan suka daga jama’a kan matakinsa na neman wa’adi na uku a Majalisar Wakilai. Ga mutane da dama a Kauru, wannan taro bai yi kama da sahihin tattaunawa da al’umma ba, sai dai yunƙurin gaggawa na rage tasirin ƙorafin da ke ƙara ƙamari a tsakanin jama’a.

Duk wani bincike ya nuna cewa taron ya fi kama da haɗuwar tsofaffin ’yan siyasa da abokan hulɗar kafafen sadarwa ta zamani, ba mu’amala ta gaskiya da al’ummar Kauru ba.

A tsarin dimokiraɗiyya, wannan bambanci yana da muhimmanci. Ana iya shirya taruka, a fitar da sanarwa, a bayyana biyayya, amma a ƙarshe ƙuri’u na jama’a a ƙauyuka, unguwanni da rumfunan zaɓe ne ke yanke hukuncin zaɓe.

Babban saƙon da aka riƙa jaddadawa a taron shi ne nuna cikakkiyar biyayya ga Gwamna Uba Sani da Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Babu shakka, biyayya ga shugabancin jam’iyya abu ne da ake tsammani. Sai dai biyayya kaɗai ba ta lashe zaɓe. Abin da ke lashe zaɓe shi ne amincewa, kuma amincewa tana samuwa ne ta hanyar aiki, kusanci da jama’a, da girmama ra’ayin masu zaɓe.

Mutanen Kauru ba sa adawa da jam’iyyar APC, haka nan ba sa adawa da gwamna. Abin da suke adawa da shi, shi ne goyon bayan shugabanci da suke ganin ba wakilce su yadda ya kamata ba.

Zaɓen Majalisar Wakilai na shekarar 2023 har yanzu yananan sabo a zukatan jama’a. A wancan zaɓe, Hon. Mukhtar Chawai bai yi nasara a rumfunan zaɓe ba, inda aka dankarashi da kasa da tazara mai yawa, kusan ƙuri’u 5,000, abin da ya nuna yanayin ra’ayin jama’a a wancan lokaci. Duk da cewa samun kujerarsa ta hannun kotu na iya kammala shari’a, bai goge ainihin gaskiyar siyasa ba. Har yanzu jama’a da dama na jin cewa an juya musu sakamakon zaɓensu, kuma wannan ra’ayi ya ci gaba da tasiri kan tunanin al’umma.

Lokacin da mutum ya hau mulki a irin wannan yanayi, tsammanin jama’a kan kasance babba. ’Yan mazaba sukan sa ran ganin aiki a fili, tsayawa tsayin daka wajen kare muradun yankin, da kuma amfanin da zai shafi al’umma kai tsaye. Abin takaici, yawancin mutanen Kauru na ganin da wahala su nuna manyan ayyuka, wakilci mai tasiri, ko kuma ci gaba da hulɗa da jama’a da za su ba da hujjar tsawaita wa’adi. Wannan tazara tsakanin tsammani da abin da aka gani ita ce ke haddasa ƙara yawan fushin jama’a a faɗin ƙaramar hukumar.

A jihar Kaduna da ma Najeriya baki ɗaya, akwai misalai bayyanannu da ke nuna cewa ingantaccen wakilci ba ya dogara da shekaru ko dogon zama a siyasa. Matasa ’yan majalisa irin su Bello El-Rufai sun nuna cewa kusanci da jama’a, jawo ayyuka masu ma’ana, da sanar da al’umma ci gaban aiki akai-akai abu ne mai yiyuwa cikin ɗan gajeren lokaci. Irin waɗannan misalai suna sa jama’a kasa karɓar uzurin gazawa.

Dalilin nan ne ya sa yunƙurin neman wa’adi na uku ke tayar da ƙarin damuwa. Neman ƙarin wa’adi ba laifi ba ne a kansa, amma dole ne ya kasance tare da manyan nasarori da karuwar amincewar jama’a. Idan babu waɗannan, irin wannan buri yana fara bayyana a matsayin son rai na kai, ba hidimar jama’a ba. Mutanen Kauru na tambaya guda mai muhimmanci: “Me ya sauya tun bayan 2023 da zai ba da hujjar sabon wa’adi?”

Ƙoƙarin jingina kai sosai da gwamna shi ma yana tayar da tambayoyi a tsakanin masu zaɓe. Gwamnoni sukan yi nasara ne idan sun yi aiki tare da ’yan takara masu cikakken goyon bayan jama’a. Jingina kai da wanda jama’a ke ganin sun ƙi a rumfunan zaɓe na iya zama barazana ta siyasa. Mutanen Kauru suna da wayewar siyasa, kuma sun saba bayyana matsayinsu a fili ta hanyar ƙuri’a.

Wannan rubutu ba hari ba ne ga Gwamna Uba Sani. Saƙo ne na gaskiya daga Jakadun Matasa na Kauru (KYA). Idan gwamnan na son samun nasara a ƙaramar hukumar Kauru, ya kamata ya saurari jama’a kai tsaye, ba kawai ta bakin ’yan siyasa masu shiga tsakani ba. Shawarwari na gaskiya a dukkan unguwanni da ƙauyuka za su tabbatar da yanayin ra’ayin jama’a. Abin da mutane ke so shi ne wakilci nagari, mai amsa kiran jama’a, kuma wanda ya fifita muradun al’umma.

Dimokiraɗiyya ta fi hukuncin kotu da tarukan jam’iyya. Ana gina ta ne kan yardar jama’a da amincewarsu. Idan shugabanni suka manta da wannan gaskiya, sukan rasa jama’a. Mutanen Kauru sun riga sun bayyana matsayinsu, kuma alamu na nuna suna shirye su sake yin hakan.

A ƙarshe, iko ba ya fitowa daga kusanci da masu mulki, yana fitowa ne daga jama’a. Ana iya bayyana biyayya a taruka, amma amincewa sai an samu ta a rumfunan zaɓe. Wannan ita ce gaskiyar da Kauru ke ci gaba da tabbatarwa.

Yusuf Zubairu/Junaidu Ishaq Maisalari 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara