Connect with us

Labarai

Eid El-Fitr: Sarkin Kauru Ya Jaddada Muhimmancin Hadin Kai da Zaman Lafiya a Tsakanin Al’umma

Published

on

Daga Yusuf Zubairu 

Sarkin Kauru, Zakari Ya’u Usman na biyu, ya yi kira ga al’ummar masarautar da ke Jihar Kaduna, da su ci gaba da tabbatar da haɗin kai, da zaman lafiya yayin gudanar da bukukuwan Sallah .

Sarkin ya yi wannan kira ne a sakon sa na Sallah da ya gabatar a ranar Juma’a, 20 ga watan Maris na shekarar 2026, bayan kammala  azumin watan Ramadan.

Ya gode wa Allah bisa bai wa Musulmi damar ganin wannan lokaci cikin ƙoshin lafiya da walwala.

Dangane da tsaro, Sarkin ya tabbatar da cewa an samu ci gaba a yankin, amma ya yi gargadin har yanzu akwai barazanar satar mutane da sauran laifuka makamantansu.

Ya bukaci al’umma da su kasance masu lura don kare yankunansu, tare da kai rahoton duk wani motsin bako a yankin.

Muhammad Sani Suleiman (Danburan)

Zakari Ya’u II ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin dukkan al’umma, ba tare da la’akari da addini ko kabilanci ba, yana mai cewa haɗin kai ne ke tabbatar da zaman lafiya da tsaro a masarautar.

Sarkin yakuma bayyana zaman lafiya a matsayin ginshiƙin ci gaba, inda ya yi gargadi kan yada jita-jita da ka iya haifar da tashe tashen hankula.

Ya kuma bukaci al’summar masarautar da su ci gaba da zama tare cikin mutunta juna da fahimtar juna.

Har ila yau, Sarkin ya  jaddada muhimmancin kula da lafiyar jama’a, inda ya bukaci su kula da tsafta, tsaftace muhalli, da kuma neman kulawar lafiya cikin gaggawa idan bukatar hakan ta taso.

Haka zalika ya yi nuni da muhimmancin rigakafin cututtuka, ciki har da allurar rigakafi na yau da kullum, musamman ga yara da mata masu juna biyu, bisa shirye-shiryen lafiyar jama’a da ake gudanarwa.

A bangaren ilimi, Sarkin Kauru ya bukaci a kara himma a fannin ilimin zamani da na addini, yana mai kira ga iyaye da matasa su fifita neman ilimi a matsayin ginshiƙin ci gaban  al’umma.

Ya kuma ba da shawarar dogaro da kai, musamman ga matasa, inda ya bukace su da su koyi sana’o’i maimakon jiran aikin gwamnati kawai, yana mai cewa yakamata arika amfani da shirye-shiryen gwamnati kamar na ƙungiyoyin manoma yadda ya kamata.

Sarkin ya yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, bisa kokarinsa na kawo ci gaba a yankin, ciki har da gina hanyoyi, shirin inganta wutar lantarki, da matakan ƙarfafa tsaro. Haka kuma ya yaba wa Shugaban Karamar Hukumar Kauru, Honarabul Bashir Tanko Dawaki, bisa jajircewarsa wajen ci gaban karkara.

Ya bukaci gwamnati ta kara himma wajen ciki gina muhimman hanyoyi da za su haɗa Kauru da sauran yankuna makwabta, da ƙarin tallafin noma ga manoma, da kuma kafa makarantar sakandare a garin Kauru.

Zakari Ya’u II ya kuma yi kira da a ci gaba da aikin gyaran Fadar Masarautar Kauru, musamman mataki na biyu.

A ƙarshe, Sarkin ya yi addu’ar samun zaman lafiya yayin bukukuwan Sallah, da ci gaba da lafiya, tare da roƙon Allah ya karɓi ibadun da aka yi a watan Ramadan.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara