Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za ta Dauki Sabbin Ma’aikata a Kananan Hukumomi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta dage takunkumin daukar ma’aikata bisa barazanar karancin ma’aikata a kananan hukumomi 27 na jihar.

Shugaban Hukumar Kula da Ayyukan Kananan Hukumomi ta Jihar Jigawa, DIG Uba Bala Ringim mai ritaya ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin da yake wa ‘yan jarida bayani kan nasarorin da hukumar ta cimma a shekarar 2025, a dakin taro na hukumar.

Ringim ya ce an dauki matakin ne sakamakon raguwar ma’aikata da aka samu a kananan hukumomi da Hukumar Ilimi ta Kananan Hukumomi (LEAs), wanda yawanci ya faru ne saboda ritaya da kuma rasuwa.

Ya bayyana cewa a shekarar 2025 kadai, hukumar ta yi wa ma’aikata 1,682 karin girma tare da shirya taruka da bitoci 163 da nufin karfafa kwarewa, ingancin aiki a matakin kananan hukumomi.

A cewarsa, ma’aikata 628 sun yi ritaya daga aiki a cikin shekarar a fadin kananan hukumomi, yayin da ma’aikata 72 na kananan hukumomi da 83 na hukumar ilimi suka rasu. Bugu da kari, ma’aikatan hukumar ilimi na kananan hukumomi 704 ma sun yi ritaya a wannan lokaci.

Yawaitar ritaya ba tare da gaggauta maye gurbi ba na ci gaba da raunana karfin tafiyar da mulki a kananan hukumomi,” in ji Ringim.

Ya bayyana cewa a halin yanzu hukumar na da ma’aikata 6,322, wanda ke nuna raguwar kusan kashi ashirin bia dari, sakamakon ritaya da rasuwa a shekarar 2025.

Ringim ya kara da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da daukar karin ma’aikatan kananan hukumomi a shekarar 2026 domin karfafa yawan ma’aikata da inganta isar da ayyuka ga al’umma a fadin kananan hukumomin jihar.

 

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara