Labarai
NIPHID Ta Kaddamar da Gangamin Wayar da Kai Kan Cutar Kuturta a Kasuwannin Jihar Kaduna
Daga Ibrahim Suleiman
Hukumar Kula da Lafiya da Cututtuka Masu Yaduwa ta Kasa (NIPHID), da ke Saye a karamar hukumar Zariya ta jihar Kaduna, ta gudanar da gangamin wayar da kan jama’a a kasuwannin Giwa da Yakawada da ke jihar, domin tunawa da Ranar Duniya ta Cutar Kuturta, tare da nufin wayar da kan jama’a game da rigakafi, gano cutar da wuri, da kuma maganinta.
A yayin gangamin, Daraktan-Janar na hukumar Abdullahi Dalhatu Aminu, ya ce an shirya aikin ne domin ilmantar da jama’a cewa cutar kuturta tana warkewa, musamman idan an gano ta da wuri.
“Alamomin cutar sun hada da canjin launin fata—fari, ja, ko baki—sau da yawa ana kuma rasa jin zafi ko sanyi a wurin da cutar ta shafa,” in ji shi.

A don haka Dr. Aminu ya bukaci jama’a da su garzaya zuwa cibiyar lafiya mafi kusa idan sun lura da canje-canje a fata, yana mai jaddada cewa gano cutar da wuri na hana nakasa da kuma hana yaduwar cutar.
Ya kara da cewa Ranar Duniya ta Cutar Kuturta tana baiwa jama’a dama su dawo da martabar wadanda cutar ta shafa da kuma yakar wariya da rashin fahimta. “Mutanen da suka kammala magani sun warke gaba daya kuma ba za su iya yada cutar ba,” in ji shi.
An zabi karamar hukumar Giwa don yin wannan gangami ne saboda kididdigar da ake da ita na nuna cewa ita ce ke da yawan rahoton cutar kuturta a jihar, in ji Dr. Aminu.
A jawabinta, Dr. Umma Aliyu, Shugabar Sashen Asibitoci a NIPHID, ta shawarci marasa lafiya da ke kan magani da su bi ka’idojin shan magungunansu yadda ya kamata domin gujewa matsaloli ko dawowar cutar.

Shi ma a nasa jawabin, Sarkin Kasuwar Giwa, Malam Ibrahim Isa, ya bukaci jama’a da su kaucewa wariya da nuna bambanci, tare da karfafa goyon baya, fahimta da tausayi ga wadanda ke fama da cutar.
Wasu daga cikin marasa lafiya, ciki har da Yarima Dalladi Paul, Malam John, da Ayuba Kom, sun raba labaran kwarewarsu tare da rokon jama’a da su daina nuna wariya ga wadanda ke da cutar.
Taron gangamin ya hada da jawabai na lafiya da tattaunawa da al’umma domin inganta wayar da kai da kuma karfafa gwiwar mutane da su garzaya asibiti da wuri idan sun lura da alamominta.
Taken Ranar Duniya ta Cutar Kuturta na wannan shekara shi ne: “Cutar Kuturta tana warkewa, babban kalubale shi ne nuna wariya.”
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
